• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labaran Kasuwanci
0
Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na uku, Makarantar ‘ARAM MAMU ACADEMY’ ta yi bikin yaye wasu daga cikin dalibanta da suka kammala aji na biyar na fannin Nursury a karkashin jagorancin darakta kuma wanda ya kafa makarantar, Muhammad Mamu Zannan Tungar Maje.

An gudanar da bikin ne a harabar makarantar da ke bayan barikin soji ta Zuba a yankin Karamar Hukumar Tafa ta Jihar Neja.

  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”
  • Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sassan Kasa Da Kasa Da Su Yi Hadin Gwiwar Samar Da Ci Gaban Duniya

Bikin ya samu halartar iyayen yara, malamai da sauran manyan baki daga sassan kasar nan.

Da yake gabatar da jawabi a yayin bikin, Dagacin Tungan Maje Salihu Isyaku, wanda shi ne uban taro, ya sanya wa makarantar albarka, inda ya ce babu abin da za a ce da wanda ya kafa wannan makaranta sai sam barka, sannan kuma ya yi addu’ar Allah ya sa shi Zannan Tungar Maje ya gida jami’a nan gaba.

“Mu dai shekarunmu sun tafi, amma dai ga fadawanmu masu tasowa, don haka ina addu’ar Allah ya sanya albarka, sannan ina gargadin jama’a mu yi zaman lafiya da juna.

Labarai Masu Nasaba

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

Domin shi wanda ya gina wannan makaranta, zama lafiyar da muka yi shi ne ya sa har na ga ya dace na ba shi sarautar Zannan Tungar Maje, domin da ba a yi zaman lafiya da shi ba ka ga da hakan ba ta samu ba, muna girmama shi muna kuma mutunta shi.

Don haka muna fatan jama’a za su zauna lafiya da juna, domin zaman lafiya ya fi komai muhimmanci,”in ji shi.

A karshe ya yi kira ga jama’a su zama masu aikata alheri domin shi ne zai taimaki mutum duniya da lahira.

Da yake bayani kan muhimmacin ilimin mata, Dakta Mamu Alhaji Muhammad, cewa ya yi “Ilimin mata dai yana da muhimmaci ko a addini, saboda a halin yanzu tarbiyyar yara ta koma hannun iyaye mata, to idan kuwa haka ne ya zama ba a tarbiyyantar da su, to za a samu nakasu a tarbiyyar da ake yi musu.

Kuma duk da cewa ana fama da matsalar tsaro bai kamata kuma ya zama dalili na kasa ilmantar da yara mata ba, saboda su ne iyayen gobe.”

A gefe guda kuma ya yi kira ga iyaye masu dora wa ‘ya’yansu talla da su nisanci yin hakan, lallai kuma su kula sosai wajen ba su kariya yadda ya kamata, sannan a tabbatar an kai su makaranta sun koyi ilimin addini da na zamani baki daya, don wannan shi ne zai taimake su wajen zaman rayuwarsu.

Shi ma Abdurrahman Abdullahi, daya daga cikin manyan baki wanda kuma amini ne ga Muhammad Mamu, cewa ya yi wannan shi ne karo na uku da ake yin gabatar da wannan biki na yaye dalibai kuma duk yana halarta.

“Wannan shi ne karo na uku da nake halartar wannan taro na yaye daliban wannan makaranta, saboda amincin da ke tsakannmu da shi, kuma da yake abu ne da ya shafi ilimi abu ne mai muhimmancin gaske, musamman ga al’ummar da suke wannan wuri, kuma zamansa a nan ya kawo alheri da albarka ganin yadda mutane suka halarci wanna wuri ya nuna irin zaman lafiya da yake yi da jama’a, kuma zuwan sarki ma kadai ya isa a fahimci cewa shi mutumin kirki ne tun da gashi ya zo ya zauna har lokacin da ake kammala wannan taro,” in ji shi.

Ya ci gaba cewa ya kamata mu kula da ilimi, domin idan ka kammala karatu ba lallai ne a ce ka samu aikin gwamnati ba, amma ilimi zai saita ka ta yadda za ka iya zama nagartacce.

Ya ce akwai bukatar iyaye su sanya ido su ga mene ne ke zuwa ya komo, hakan kuwa yana da alaka da jituwarsu da malamai, su rika jan su a jiki suna sanin halin da karatunsu ‘ya’yansu ke ciki.

Tun farko, Daraktan makarantar, wanda kuma shi ne ya assasa ta, Muhammad Mamu, Zannan Tungar Maje, cewa ya yi wannan shi ne yaye dalibai na farko daga nazirin farko zuwa firamare, amma daga firamare ta daya zuwa wannan shi ne karo na uku jimilla.

 “Kuma wannan makaranta tana da dalibai kusan 200, ni kadai ke daukar nauyin makarantar sai kuma yayyena da suke tallafa min. Ina kira ga gwamnati ta shigo cikin al’amarin makarantu masu zaman kansu, domin makarantu masu zaman kansu na taimaka wa gwamnati kwarai wajen sama wa mutane aikin yi da kuma hanyar rage yawan dalibai.

 “To idan aka samu marantu da suke da hazaka wajen koyarwa da tarbiyyantar da yara, ya kamata gwamnati ta shigo ta tallafa wajen gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnati da dage wajen tabbatar da tsaron al’umma da dukiyoyinsu.

Ita ma malama a makarantar kuma uwargida ga Muhammad Mamu, ta nuna farin cikinta bisa ga yadda yara suka nuna bajinta wajen bayyana abubuwan da aka koya musu.

Ta bayyana matakin karbar yara daga gidanjen iyayensu zuwa makaranta da kuma bayan an tashi, inda ta ce, iyaye suna sanya hannu yayin da aka je dauko ‘ya’yansu a motar makarantar da kuma bayan an hannanta su ga iyayensu a ko da yaushe, domin tabbatar da tsaro da lafiyarsu.

An gabatar da dalibai ‘yan shekaru 10 zuwa 13, wadanda suka nuna bajinta wajen gabatar da shirye-shirye a harshen Turanci, kafin daga baya aka gabatar da shiri na al’adun gargajiya na kabilu daban-daban domin kayatar da manyan baki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aram Mamu AcademyCiniki Da KasuwanciMakaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ba Za Ta Taba Maimaita Yakin Basasa Na Shekarar 1967 —el-Rufai

Next Post

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

Related

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

5 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

6 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

9 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

9 months ago
Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci
Labaran Kasuwanci

Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci

11 months ago
Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 
Labaran Kasuwanci

Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 

11 months ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Makarantar

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.