ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Makarantar

A karo na uku, Makarantar ‘ARAM MAMU ACADEMY’ ta yi bikin yaye wasu daga cikin dalibanta da suka kammala aji na biyar na fannin Nursury a karkashin jagorancin darakta kuma wanda ya kafa makarantar, Muhammad Mamu Zannan Tungar Maje.

An gudanar da bikin ne a harabar makarantar da ke bayan barikin soji ta Zuba a yankin Karamar Hukumar Tafa ta Jihar Neja.

  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”
  • Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sassan Kasa Da Kasa Da Su Yi Hadin Gwiwar Samar Da Ci Gaban Duniya

Bikin ya samu halartar iyayen yara, malamai da sauran manyan baki daga sassan kasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake gabatar da jawabi a yayin bikin, Dagacin Tungan Maje Salihu Isyaku, wanda shi ne uban taro, ya sanya wa makarantar albarka, inda ya ce babu abin da za a ce da wanda ya kafa wannan makaranta sai sam barka, sannan kuma ya yi addu’ar Allah ya sa shi Zannan Tungar Maje ya gida jami’a nan gaba.

“Mu dai shekarunmu sun tafi, amma dai ga fadawanmu masu tasowa, don haka ina addu’ar Allah ya sanya albarka, sannan ina gargadin jama’a mu yi zaman lafiya da juna.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Domin shi wanda ya gina wannan makaranta, zama lafiyar da muka yi shi ne ya sa har na ga ya dace na ba shi sarautar Zannan Tungar Maje, domin da ba a yi zaman lafiya da shi ba ka ga da hakan ba ta samu ba, muna girmama shi muna kuma mutunta shi.

Don haka muna fatan jama’a za su zauna lafiya da juna, domin zaman lafiya ya fi komai muhimmanci,”in ji shi.

A karshe ya yi kira ga jama’a su zama masu aikata alheri domin shi ne zai taimaki mutum duniya da lahira.

Da yake bayani kan muhimmacin ilimin mata, Dakta Mamu Alhaji Muhammad, cewa ya yi “Ilimin mata dai yana da muhimmaci ko a addini, saboda a halin yanzu tarbiyyar yara ta koma hannun iyaye mata, to idan kuwa haka ne ya zama ba a tarbiyyantar da su, to za a samu nakasu a tarbiyyar da ake yi musu.

Kuma duk da cewa ana fama da matsalar tsaro bai kamata kuma ya zama dalili na kasa ilmantar da yara mata ba, saboda su ne iyayen gobe.”

A gefe guda kuma ya yi kira ga iyaye masu dora wa ‘ya’yansu talla da su nisanci yin hakan, lallai kuma su kula sosai wajen ba su kariya yadda ya kamata, sannan a tabbatar an kai su makaranta sun koyi ilimin addini da na zamani baki daya, don wannan shi ne zai taimake su wajen zaman rayuwarsu.

Shi ma Abdurrahman Abdullahi, daya daga cikin manyan baki wanda kuma amini ne ga Muhammad Mamu, cewa ya yi wannan shi ne karo na uku da ake yin gabatar da wannan biki na yaye dalibai kuma duk yana halarta.

“Wannan shi ne karo na uku da nake halartar wannan taro na yaye daliban wannan makaranta, saboda amincin da ke tsakannmu da shi, kuma da yake abu ne da ya shafi ilimi abu ne mai muhimmancin gaske, musamman ga al’ummar da suke wannan wuri, kuma zamansa a nan ya kawo alheri da albarka ganin yadda mutane suka halarci wanna wuri ya nuna irin zaman lafiya da yake yi da jama’a, kuma zuwan sarki ma kadai ya isa a fahimci cewa shi mutumin kirki ne tun da gashi ya zo ya zauna har lokacin da ake kammala wannan taro,” in ji shi.

Ya ci gaba cewa ya kamata mu kula da ilimi, domin idan ka kammala karatu ba lallai ne a ce ka samu aikin gwamnati ba, amma ilimi zai saita ka ta yadda za ka iya zama nagartacce.

Ya ce akwai bukatar iyaye su sanya ido su ga mene ne ke zuwa ya komo, hakan kuwa yana da alaka da jituwarsu da malamai, su rika jan su a jiki suna sanin halin da karatunsu ‘ya’yansu ke ciki.

Tun farko, Daraktan makarantar, wanda kuma shi ne ya assasa ta, Muhammad Mamu, Zannan Tungar Maje, cewa ya yi wannan shi ne yaye dalibai na farko daga nazirin farko zuwa firamare, amma daga firamare ta daya zuwa wannan shi ne karo na uku jimilla.

 “Kuma wannan makaranta tana da dalibai kusan 200, ni kadai ke daukar nauyin makarantar sai kuma yayyena da suke tallafa min. Ina kira ga gwamnati ta shigo cikin al’amarin makarantu masu zaman kansu, domin makarantu masu zaman kansu na taimaka wa gwamnati kwarai wajen sama wa mutane aikin yi da kuma hanyar rage yawan dalibai.

 “To idan aka samu marantu da suke da hazaka wajen koyarwa da tarbiyyantar da yara, ya kamata gwamnati ta shigo ta tallafa wajen gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnati da dage wajen tabbatar da tsaron al’umma da dukiyoyinsu.

Ita ma malama a makarantar kuma uwargida ga Muhammad Mamu, ta nuna farin cikinta bisa ga yadda yara suka nuna bajinta wajen bayyana abubuwan da aka koya musu.

Ta bayyana matakin karbar yara daga gidanjen iyayensu zuwa makaranta da kuma bayan an tashi, inda ta ce, iyaye suna sanya hannu yayin da aka je dauko ‘ya’yansu a motar makarantar da kuma bayan an hannanta su ga iyayensu a ko da yaushe, domin tabbatar da tsaro da lafiyarsu.

An gabatar da dalibai ‘yan shekaru 10 zuwa 13, wadanda suka nuna bajinta wajen gabatar da shirye-shirye a harshen Turanci, kafin daga baya aka gabatar da shiri na al’adun gargajiya na kabilu daban-daban domin kayatar da manyan baki.

Makarantar
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.