ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Makarantar

A karo na uku, Makarantar ‘ARAM MAMU ACADEMY’ ta yi bikin yaye wasu daga cikin dalibanta da suka kammala aji na biyar na fannin Nursury a karkashin jagorancin darakta kuma wanda ya kafa makarantar, Muhammad Mamu Zannan Tungar Maje.

An gudanar da bikin ne a harabar makarantar da ke bayan barikin soji ta Zuba a yankin Karamar Hukumar Tafa ta Jihar Neja.

  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”
  • Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sassan Kasa Da Kasa Da Su Yi Hadin Gwiwar Samar Da Ci Gaban Duniya

Bikin ya samu halartar iyayen yara, malamai da sauran manyan baki daga sassan kasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake gabatar da jawabi a yayin bikin, Dagacin Tungan Maje Salihu Isyaku, wanda shi ne uban taro, ya sanya wa makarantar albarka, inda ya ce babu abin da za a ce da wanda ya kafa wannan makaranta sai sam barka, sannan kuma ya yi addu’ar Allah ya sa shi Zannan Tungar Maje ya gida jami’a nan gaba.

“Mu dai shekarunmu sun tafi, amma dai ga fadawanmu masu tasowa, don haka ina addu’ar Allah ya sanya albarka, sannan ina gargadin jama’a mu yi zaman lafiya da juna.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Domin shi wanda ya gina wannan makaranta, zama lafiyar da muka yi shi ne ya sa har na ga ya dace na ba shi sarautar Zannan Tungar Maje, domin da ba a yi zaman lafiya da shi ba ka ga da hakan ba ta samu ba, muna girmama shi muna kuma mutunta shi.

Don haka muna fatan jama’a za su zauna lafiya da juna, domin zaman lafiya ya fi komai muhimmanci,”in ji shi.

A karshe ya yi kira ga jama’a su zama masu aikata alheri domin shi ne zai taimaki mutum duniya da lahira.

Da yake bayani kan muhimmacin ilimin mata, Dakta Mamu Alhaji Muhammad, cewa ya yi “Ilimin mata dai yana da muhimmaci ko a addini, saboda a halin yanzu tarbiyyar yara ta koma hannun iyaye mata, to idan kuwa haka ne ya zama ba a tarbiyyantar da su, to za a samu nakasu a tarbiyyar da ake yi musu.

Kuma duk da cewa ana fama da matsalar tsaro bai kamata kuma ya zama dalili na kasa ilmantar da yara mata ba, saboda su ne iyayen gobe.”

A gefe guda kuma ya yi kira ga iyaye masu dora wa ‘ya’yansu talla da su nisanci yin hakan, lallai kuma su kula sosai wajen ba su kariya yadda ya kamata, sannan a tabbatar an kai su makaranta sun koyi ilimin addini da na zamani baki daya, don wannan shi ne zai taimake su wajen zaman rayuwarsu.

Shi ma Abdurrahman Abdullahi, daya daga cikin manyan baki wanda kuma amini ne ga Muhammad Mamu, cewa ya yi wannan shi ne karo na uku da ake yin gabatar da wannan biki na yaye dalibai kuma duk yana halarta.

“Wannan shi ne karo na uku da nake halartar wannan taro na yaye daliban wannan makaranta, saboda amincin da ke tsakannmu da shi, kuma da yake abu ne da ya shafi ilimi abu ne mai muhimmancin gaske, musamman ga al’ummar da suke wannan wuri, kuma zamansa a nan ya kawo alheri da albarka ganin yadda mutane suka halarci wanna wuri ya nuna irin zaman lafiya da yake yi da jama’a, kuma zuwan sarki ma kadai ya isa a fahimci cewa shi mutumin kirki ne tun da gashi ya zo ya zauna har lokacin da ake kammala wannan taro,” in ji shi.

Ya ci gaba cewa ya kamata mu kula da ilimi, domin idan ka kammala karatu ba lallai ne a ce ka samu aikin gwamnati ba, amma ilimi zai saita ka ta yadda za ka iya zama nagartacce.

Ya ce akwai bukatar iyaye su sanya ido su ga mene ne ke zuwa ya komo, hakan kuwa yana da alaka da jituwarsu da malamai, su rika jan su a jiki suna sanin halin da karatunsu ‘ya’yansu ke ciki.

Tun farko, Daraktan makarantar, wanda kuma shi ne ya assasa ta, Muhammad Mamu, Zannan Tungar Maje, cewa ya yi wannan shi ne yaye dalibai na farko daga nazirin farko zuwa firamare, amma daga firamare ta daya zuwa wannan shi ne karo na uku jimilla.

 “Kuma wannan makaranta tana da dalibai kusan 200, ni kadai ke daukar nauyin makarantar sai kuma yayyena da suke tallafa min. Ina kira ga gwamnati ta shigo cikin al’amarin makarantu masu zaman kansu, domin makarantu masu zaman kansu na taimaka wa gwamnati kwarai wajen sama wa mutane aikin yi da kuma hanyar rage yawan dalibai.

 “To idan aka samu marantu da suke da hazaka wajen koyarwa da tarbiyyantar da yara, ya kamata gwamnati ta shigo ta tallafa wajen gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnati da dage wajen tabbatar da tsaron al’umma da dukiyoyinsu.

Ita ma malama a makarantar kuma uwargida ga Muhammad Mamu, ta nuna farin cikinta bisa ga yadda yara suka nuna bajinta wajen bayyana abubuwan da aka koya musu.

Ta bayyana matakin karbar yara daga gidanjen iyayensu zuwa makaranta da kuma bayan an tashi, inda ta ce, iyaye suna sanya hannu yayin da aka je dauko ‘ya’yansu a motar makarantar da kuma bayan an hannanta su ga iyayensu a ko da yaushe, domin tabbatar da tsaro da lafiyarsu.

An gabatar da dalibai ‘yan shekaru 10 zuwa 13, wadanda suka nuna bajinta wajen gabatar da shirye-shirye a harshen Turanci, kafin daga baya aka gabatar da shiri na al’adun gargajiya na kabilu daban-daban domin kayatar da manyan baki.

Makarantar
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.