• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Ware Wa Mata Kaso 35 Na Gurbin Aiki A Hukumomin Tsaro

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Mun yi maraba da ware wa mata kashi 35 cikin 100 na daukar ma’aikata a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da suka hada da jami’an tsaron (NSCDC) da Hukumar Kashe Gobara Ta Tarayya, da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, da kuma Hukumar Kula da Gyaran Hali ta Kasa.

Wannan ba karamin taimaka wa mata aka yi ba wajen basu gurbin wani kaso na aikin tsaro, saboda da yawa mata suna fama da rashi aiki yi sun gama makaranta babu aikin yi babu aure, sannan kuma babu sana’ar yi sun zama kamar zauna gari banza saboda babu abin da mutum yake yi, wata ma tana son fara sana’a amma babu kudin da za ta yi sana’a.

  • Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi
  • Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Lalle wannan ba karamin taimaka wa mata wadanda ba sa aiki aka yi ba, saboda za su samu abin yi sannan kuma za su samu abin da za su rika rufa wa kansu asiri kila har su taimakawa wani.

Sannan zai rage musu yawace-yawace da shiririta da zaman rashi aikin yi da yawan gulmace-gulmace duk wadannan zai rage dama rashin aikin yi ne yake kawo su. Sannan kuma mata za su ci gaba da samun karfin gwiwar yin karatu saboda sun san idan sun gama za su samu aiki, domin rashin aikin yi ba karamin kashe wa mutum gwiwa yake ba, mutum zai sha wahalar karatu, kudin makaranta, kudin takardun karatu da ‘yan cemi-cemi, sannan kuma mutum ya gama babu aiki wannan bakaramin wahala ake ba.

Mata na fuskanta kalubale wajen daukar su aiki za ku ga mata suna yawon neman aiki amma kuma ba sa samu wasu ma a yi ta musu wasa da hankali, wasu ma idan suka hadu da mutumin banza ya nemi ya bata musu rayuwa sai a ce sai mace ta yarda da shi sannan ya bata aiki, to gaskiya wannan ba karamin kalubale bane a ce sai mace ta rasa mutuncinta sannan a bata aiki, wata kuma tana samun kalubale ne daga wajen mijinta wasu mazajen suna hana mata aiki, ko kuma idan an barta ta yi aikin za su rika samun matsala, wasu kuma dama suke dauke da dauyin kansu, wasu kuma mazajen suna sa musu idon akan abin da suka samu.

Wannan shi ne kalubalen da mata suke fukanta a harkar aiki. Don haka yana da kyau mata mu ci moriyar aikinmu ta hanyar rike aikinmu tsakaninmu da Allah babu cuta babu cutarwa ina ganin idan muka tsarkake zuciyarmu za mu ci moriyar abin bamu kadai ba har da ma wasunmu.

Yana da kyau mata mu kiyaye mutuncimmu sannan kuma mu kama kammu, ki sani ke mace ce a wajen aiki da yawan mazaje abin da ya sa suke hana matansu aiki kenan saboda rashin kamun kai, mata mu yi kokarin kiyaye kanmu sai ki ga an yi kokarin kiyaye hakkin ki a wajen aiki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami’an Yada Labarai A Kano

Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami'an Yada Labarai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.