• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Ware Wa Mata Kaso 35 Na Gurbin Aiki A Hukumomin Tsaro

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Rahotonni
0
Maraba Da Ware Wa Mata Kaso 35 Na Gurbin Aiki A Hukumomin Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Mun yi maraba da ware wa mata kashi 35 cikin 100 na daukar ma’aikata a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da suka hada da jami’an tsaron (NSCDC) da Hukumar Kashe Gobara Ta Tarayya, da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, da kuma Hukumar Kula da Gyaran Hali ta Kasa.

Wannan ba karamin taimaka wa mata aka yi ba wajen basu gurbin wani kaso na aikin tsaro, saboda da yawa mata suna fama da rashi aiki yi sun gama makaranta babu aikin yi babu aure, sannan kuma babu sana’ar yi sun zama kamar zauna gari banza saboda babu abin da mutum yake yi, wata ma tana son fara sana’a amma babu kudin da za ta yi sana’a.

  • Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi
  • Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Lalle wannan ba karamin taimaka wa mata wadanda ba sa aiki aka yi ba, saboda za su samu abin yi sannan kuma za su samu abin da za su rika rufa wa kansu asiri kila har su taimakawa wani.

Sannan zai rage musu yawace-yawace da shiririta da zaman rashi aikin yi da yawan gulmace-gulmace duk wadannan zai rage dama rashin aikin yi ne yake kawo su. Sannan kuma mata za su ci gaba da samun karfin gwiwar yin karatu saboda sun san idan sun gama za su samu aiki, domin rashin aikin yi ba karamin kashe wa mutum gwiwa yake ba, mutum zai sha wahalar karatu, kudin makaranta, kudin takardun karatu da ‘yan cemi-cemi, sannan kuma mutum ya gama babu aiki wannan bakaramin wahala ake ba.

Mata na fuskanta kalubale wajen daukar su aiki za ku ga mata suna yawon neman aiki amma kuma ba sa samu wasu ma a yi ta musu wasa da hankali, wasu ma idan suka hadu da mutumin banza ya nemi ya bata musu rayuwa sai a ce sai mace ta yarda da shi sannan ya bata aiki, to gaskiya wannan ba karamin kalubale bane a ce sai mace ta rasa mutuncinta sannan a bata aiki, wata kuma tana samun kalubale ne daga wajen mijinta wasu mazajen suna hana mata aiki, ko kuma idan an barta ta yi aikin za su rika samun matsala, wasu kuma dama suke dauke da dauyin kansu, wasu kuma mazajen suna sa musu idon akan abin da suka samu.

Wannan shi ne kalubalen da mata suke fukanta a harkar aiki. Don haka yana da kyau mata mu ci moriyar aikinmu ta hanyar rike aikinmu tsakaninmu da Allah babu cuta babu cutarwa ina ganin idan muka tsarkake zuciyarmu za mu ci moriyar abin bamu kadai ba har da ma wasunmu.

Yana da kyau mata mu kiyaye mutuncimmu sannan kuma mu kama kammu, ki sani ke mace ce a wajen aiki da yawan mazaje abin da ya sa suke hana matansu aiki kenan saboda rashin kamun kai, mata mu yi kokarin kiyaye kanmu sai ki ga an yi kokarin kiyaye hakkin ki a wajen aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilai 20 Da Ke Sa Dalibai Faduwa Jarrabawa (5)

Next Post

Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami’an Yada Labarai A Kano

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

3 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

3 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

4 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

4 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 month ago
Next Post
Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami’an Yada Labarai A Kano

Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami'an Yada Labarai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.