ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Ware Wa Mata Kaso 35 Na Gurbin Aiki A Hukumomin Tsaro

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Mun yi maraba da ware wa mata kashi 35 cikin 100 na daukar ma’aikata a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da suka hada da jami’an tsaron (NSCDC) da Hukumar Kashe Gobara Ta Tarayya, da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, da kuma Hukumar Kula da Gyaran Hali ta Kasa.

Wannan ba karamin taimaka wa mata aka yi ba wajen basu gurbin wani kaso na aikin tsaro, saboda da yawa mata suna fama da rashi aiki yi sun gama makaranta babu aikin yi babu aure, sannan kuma babu sana’ar yi sun zama kamar zauna gari banza saboda babu abin da mutum yake yi, wata ma tana son fara sana’a amma babu kudin da za ta yi sana’a.

  • Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi
  • Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Lalle wannan ba karamin taimaka wa mata wadanda ba sa aiki aka yi ba, saboda za su samu abin yi sannan kuma za su samu abin da za su rika rufa wa kansu asiri kila har su taimakawa wani.

Sannan zai rage musu yawace-yawace da shiririta da zaman rashi aikin yi da yawan gulmace-gulmace duk wadannan zai rage dama rashin aikin yi ne yake kawo su. Sannan kuma mata za su ci gaba da samun karfin gwiwar yin karatu saboda sun san idan sun gama za su samu aiki, domin rashin aikin yi ba karamin kashe wa mutum gwiwa yake ba, mutum zai sha wahalar karatu, kudin makaranta, kudin takardun karatu da ‘yan cemi-cemi, sannan kuma mutum ya gama babu aiki wannan bakaramin wahala ake ba.

Mata na fuskanta kalubale wajen daukar su aiki za ku ga mata suna yawon neman aiki amma kuma ba sa samu wasu ma a yi ta musu wasa da hankali, wasu ma idan suka hadu da mutumin banza ya nemi ya bata musu rayuwa sai a ce sai mace ta yarda da shi sannan ya bata aiki, to gaskiya wannan ba karamin kalubale bane a ce sai mace ta rasa mutuncinta sannan a bata aiki, wata kuma tana samun kalubale ne daga wajen mijinta wasu mazajen suna hana mata aiki, ko kuma idan an barta ta yi aikin za su rika samun matsala, wasu kuma dama suke dauke da dauyin kansu, wasu kuma mazajen suna sa musu idon akan abin da suka samu.

Wannan shi ne kalubalen da mata suke fukanta a harkar aiki. Don haka yana da kyau mata mu ci moriyar aikinmu ta hanyar rike aikinmu tsakaninmu da Allah babu cuta babu cutarwa ina ganin idan muka tsarkake zuciyarmu za mu ci moriyar abin bamu kadai ba har da ma wasunmu.

Yana da kyau mata mu kiyaye mutuncimmu sannan kuma mu kama kammu, ki sani ke mace ce a wajen aiki da yawan mazaje abin da ya sa suke hana matansu aiki kenan saboda rashin kamun kai, mata mu yi kokarin kiyaye kanmu sai ki ga an yi kokarin kiyaye hakkin ki a wajen aiki.

Tsaro
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Tsaro
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Tsaro
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami’an Yada Labarai A Kano

Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami'an Yada Labarai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.