ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Ware Wa Mata Kaso 35 Na Gurbin Aiki A Hukumomin Tsaro

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Mun yi maraba da ware wa mata kashi 35 cikin 100 na daukar ma’aikata a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da suka hada da jami’an tsaron (NSCDC) da Hukumar Kashe Gobara Ta Tarayya, da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, da kuma Hukumar Kula da Gyaran Hali ta Kasa.

Wannan ba karamin taimaka wa mata aka yi ba wajen basu gurbin wani kaso na aikin tsaro, saboda da yawa mata suna fama da rashi aiki yi sun gama makaranta babu aikin yi babu aure, sannan kuma babu sana’ar yi sun zama kamar zauna gari banza saboda babu abin da mutum yake yi, wata ma tana son fara sana’a amma babu kudin da za ta yi sana’a.

  • Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi
  • Xi Ya Bukaci Sin Da Faransa Su Hada Hannu Wajen Bude Hanyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Domin Kyautata Rayuwar Bil Adama

Lalle wannan ba karamin taimaka wa mata wadanda ba sa aiki aka yi ba, saboda za su samu abin yi sannan kuma za su samu abin da za su rika rufa wa kansu asiri kila har su taimakawa wani.

Sannan zai rage musu yawace-yawace da shiririta da zaman rashi aikin yi da yawan gulmace-gulmace duk wadannan zai rage dama rashin aikin yi ne yake kawo su. Sannan kuma mata za su ci gaba da samun karfin gwiwar yin karatu saboda sun san idan sun gama za su samu aiki, domin rashin aikin yi ba karamin kashe wa mutum gwiwa yake ba, mutum zai sha wahalar karatu, kudin makaranta, kudin takardun karatu da ‘yan cemi-cemi, sannan kuma mutum ya gama babu aiki wannan bakaramin wahala ake ba.

Mata na fuskanta kalubale wajen daukar su aiki za ku ga mata suna yawon neman aiki amma kuma ba sa samu wasu ma a yi ta musu wasa da hankali, wasu ma idan suka hadu da mutumin banza ya nemi ya bata musu rayuwa sai a ce sai mace ta yarda da shi sannan ya bata aiki, to gaskiya wannan ba karamin kalubale bane a ce sai mace ta rasa mutuncinta sannan a bata aiki, wata kuma tana samun kalubale ne daga wajen mijinta wasu mazajen suna hana mata aiki, ko kuma idan an barta ta yi aikin za su rika samun matsala, wasu kuma dama suke dauke da dauyin kansu, wasu kuma mazajen suna sa musu idon akan abin da suka samu.

Wannan shi ne kalubalen da mata suke fukanta a harkar aiki. Don haka yana da kyau mata mu ci moriyar aikinmu ta hanyar rike aikinmu tsakaninmu da Allah babu cuta babu cutarwa ina ganin idan muka tsarkake zuciyarmu za mu ci moriyar abin bamu kadai ba har da ma wasunmu.

Yana da kyau mata mu kiyaye mutuncimmu sannan kuma mu kama kammu, ki sani ke mace ce a wajen aiki da yawan mazaje abin da ya sa suke hana matansu aiki kenan saboda rashin kamun kai, mata mu yi kokarin kiyaye kanmu sai ki ga an yi kokarin kiyaye hakkin ki a wajen aiki.

Tsaro
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami’an Yada Labarai A Kano

Dantiye Ya Bukaci Samun Karin Hadin Kai Tsakanin Jami'an Yada Labarai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.