• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

…Zai Ci Amanar APC Ba Da Jimawa Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamba a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Dakta Don Pedro Obaseki ya bayyana cewa ministan Abuja kuma tsohon gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya ketare iyaka na kiran a dakatar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Idan za a iya tunawa a wata tattaunawa da aka yi da Wike a gidan talabijin na Channels a shirin siyasa a yau, ya bayyana cewa, “Duba da wuraren da PDP ta yi rashin nasara saboda girman kai da kwadayi da kuma rashin adalci. Idan da PDP ta yi abin da ya kamata ta yi, to da ba wannan maganan ake ba a yanzu.

  • Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Cardoso A Matsayin Sabon Gwamnan CBN

“Ya kamata a ce an yi adalci, wanda hakan ya sa nake kira da kwamitin gudanar-wa na jam’iyyar ya dakatar da dan takarar shugaban kasa da sauran wasu mutane kamar irin su Aminu Tambuwal domin sake gina jam’iyyar PDP.”

Sai dai da yake mayar da martani a gaban ‘yan jarida a Abuja, Obaseki ya ce jiga-jigan jam’iyya mai mulki ta APC su shirya amsar cin amana daga wurin Wike, inda ya ce PDP ba za ta iya ci gaba da lamuntar duk wani cin kashi daga hannun Wike ba.

Ya ce, “Shi ne mafic in amanan jam’iyyar a tarihin siyasarmu. Ya raba gari da Ro-timi Amaechi da Goodluck Jonathan da Peter Odili da Atiku Abubakar, inda a yan-zu yake tare da Bola Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Wike ya fito fili ya bukaci a dakatar da shugaban jam’iyyarmu na kasa kuma dan takarar shugaban kasa na tutar jam’iyyar, wanda ‘yan Nijeriya suka amshe shi hannu bibiyu kamar yadda INEC ta gabatar da cewa mun lashe jihohi 21, sannan har ya nemi a dakatar da Atiku daga jam’iyyar, lallai Wike ya ketare iya a halin yanzu, ya kamata ya shirya yaki.

“Yana da kudin da zai iya yaki da mu, saboda muna zuwa gare shi kamar runduna. Na tabbata Wike ya karaci fannin shari’a. Na tabbata shi lauya ne kuma ya san cewa duk mai shirin zaman lafiya dole ya shirya wa yaki.

“Nyesom Wike ya tabo tsuliyar dodo, ya jira ya ga abin da zai same shi. Shawarar kawai da zan bayar ita ce, wadanda suka hada baki da shi suka ci amana wajen yi wa APC aiki, su jira karshensu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Obaseki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

Next Post

Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

11 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Wike
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Wike

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.