• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Daina Yawace-yawace Da Shige-shige Mara Amfani -Halima Kassim

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
in Rahotonni
0
Mata A Daina Yawace-yawace Da Shige-shige Mara Amfani -Halima Kassim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

HALIMA KASSIM, hazika ce kuma jajirtacciya mai neman na kanta, ta yi jan hankali ga mata kan su yi biyayya ga mazajensu, su nemi halal, sannan su tsaya wuri guda domin kare mutuncinsu da na iyaye kai har ma da na ‘ya’yan da za su haifa. Haka nan ta shawarce su da su kiyaye yawace-yawace da yawan shige-shige marasa amfani.

Halima ta yi wannan jan hankali ne a tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM. Ga dai yadda ta kasance a tsakaninsu:

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin

Da fari za mu so sanin cikekken sunanki da tarihinki?

Assalamu alaikum warahmatullah. Sunana Halima Kassim, an haife ni a Karamar Hukumar Hadejia Jihar Jigawa. Na yi makarantar firamare a ‘Abdulkadir Special Primary School Hadejia,’ daga nan kuma bayan na gama na tafi Women Teachers College Malammadori, na yi J S S 1,2,3 daga nan na tafi Science Secondary School Jahun na yi S S S 1,2,3.na gama karatuna na secondary.

Shin Hajiya Halima matar aure ce ko kuwa?

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Eh to a yanzu dai ba ni da aure bayan na gama sikandire na yi aure ina tare da mijina cikin jin dadi da kwanciyar hankali ya amsa kiran Ubangijinsa wato Allah ya yi masa rasuwa sakamako hatsarin mota an tura shi aiki a hanyarsa ta tafiya.

Shin kun haihu da shi kafin ya rasu ko kuma baku haihu ba?

Eh Allah ya azirta mu da da daya.

Bayan rasuwarsa ba ki sake wani auren ba?

Bayan na gama takaba sai na koma karatu na yi Diploma a Enbironment Menegment, sannan kuma da na samu kamar shekaru uku a tsakani na sake komawa makaranta na yi National Diploma For History yanzu kuma ina H .N.D. na kusa gamawa.

To Hajiya Halima idan kin gama HND za ki ci gaba ne da karatu ko kuma za ki yi aure?

Eh, duk wanda ya samu zan yi in sha Allahu in aure ne muna fatan Allah ya kawo miji nigari.

Hajiya Halima, duk karatun nan da kike yi kina aiki ne ko kuma karatun ne kike ta yi?

Eh to da lokacin ina gidan mijina na samu aiki ina dan yi a Local Gobernment, to tun da Allah yai masa rasuwa na dawo gidammu kara tun dai nake yi sai dai kuma ina taba kasuwanci haka.

Me kasuwanci naki ya kunsa?

Ina sayar da kamar akwai keken dinki da turaren wuta takalma da kayayyaki haka.

Mene ne ya ja hankalin ki kika fada kasuwanci, bayan ga karatu da kike yi?

To neman kudi ai ya zama dole a wannan rayuwar tamu ba sai ka je kana karamar murya kana ruko ba idan kana dan kasuwancin ka za ka rufa wa kanka asiri har ka taimaki wani ma, sannan za ka iya daukar dawainiyar kanka ba za ka nemi kudi a hannunka ka rasa ba, sannan a wajen karatumma za ka samu ciniki sosai to kin ga ka hada abu biyu kenan za ka ci riba biyu.

A zamanki na aure shin kin taba fuskatar wani kalubale kin san rayuwar zaman aure sai hakuri kafin maigida ya rasu?

Eh to ai ba za ka ce komai ba ita dama rayuwa zo mu zauna zo mu saba ce amma dai ni tsakani na da shi babu wani abu da ya taba shiga tsakanina da shi wanda za a ce wai gashi har an shiga tsakaninmu ko kuma wai gida su ji zama muke na nutsu da kwanciyar hankali saboda mutum ne mai kirki da gaskiya da rikon amana babu macen da za ta ce ta same shi a matsayin miji baji dadin zama da shi ba fatana shi ne Allah ya jikan sa da rahma.

To a harkar kasuwanci ki fa ba ki taba samun wani kalubale ba?

Kana kasuwanci ai ba za ka ce baka samu kalubale ba saboda akwai harkar bashi wani zai dau kayanka kafin ya ba ka kudin sai ya wahalar da kai, wani kuma sai ranka ya baci wani ba zai baka kudin ba haka zaka hakura ka barshi, dama haka kasuwanci ya kunsa akwai riba akwai kuma rashin riba sannan akwai faduwa akwai asara sai na ce ni kam Alhamdulillah.

Zuwa yanzu wace irin nasara kika samu a kasuwancinki?

To Alhamdulillah, gaskiya na samu nasarori dama gaskiya ina iya daukar kaina da har ma na taimakawa wani to kinga sai dai na ce Alhamdulillah nasarori na same su da yawa ba zan ma iya kirga su ba gaskiya sai godiya.

Wanne irin addu,a ne idan akayi miki kike jin dadi?

Addu’a duk addu’a ce, kuma duk addu’ar da aka yi maka za ka ji dadi mana har ma a ce Allah yai maka albarka da zuri’a baki daya.

Ada can kafin yanzu mene ne burinki?

A gaskiya ina da burin zama likita na yi ta kokarin hakan amma kin san kana naka Allah yana nasa kuma na Allah shi ne daidai Allah ya sa haka shi ya fi zama alkhairi.

Ga karatu ga kasuwanci ga kuma kula da danki da kika ce an bar miki, ta ya ya kike gudanar da hutunki?

Kasuwanci ai baya hana hutu, sannan kuma karatu ma shi ma idan an yi hutu zan samu na huta, daya kuma ba zai hana ni hutu ba.

Wane irin kwarin kwiwa kike samu a wajen iyaye a kan harkar karatunki da kuma kasuwanci ki?

Alhamdulillah ina samun kwarin kwiwa sosai a wajen iyaye tun suna da rai shi ya sa bayan sun rasu ma ban gajiya ba daga kasuwanci har karatu.

Kawaye fa?

To ni dai gaskiya bani da wata takamaimiyar kawa saboda mu gidammu ba,a fita daga makaranta sai gida sannan mu a tsarin gidammu mun saba da kulle, saboda mu gidammu ko aikin ka aka yi babammu yana kofar gida zai tambaye ka ina za ka idan ka ce aikenka aka yi zai ce ka koma gida a aiki namiji to shi ya sa to shi ya sa ma za ki ga bamu da kawaye.

A karshe wacce irin shawara za ki ba ‘yan ‘uwanki mata?

Shawarar da zan ba wa ‘yan uwana mata duk inda ‘ya mace take ta tsare kanta, sannan kuma ta kiyaye duk wani abubuwa da zai jawo mata matsala a rayuwar ta, ta ji tsoron Allah kuma ta kare kanta da mutunci ta da mutuncin iyayenta ta yi wa kanta mutunci ta bar yawaceyawace da shige-shige, sannan kuma mutum ya tsaya a waje daya ya kama sana’a kar ka ce za ka dogara da wani saboda dogaro da wani ba abu ne tabbatacce ba saboda Allah kadai ne za ka dogara da shi mutum idan ka dogara da wata ran akwai gajiyawa.

Wannan ita ce shawarar da zan ba wa ‘yan’uwana mata, sannan kuma a yi zaman aure a bi miji sau da kafa saboda aljannarki tana karkashi kafar mijinki .


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariHalimaHiraMataMazaShawaraTattaunawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

Next Post

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa (3)

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 week ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

1 week ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa (3)

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa (3)

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.