• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Daina Yawace-yawace Da Shige-shige Mara Amfani -Halima Kassim

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
Mata

HALIMA KASSIM, hazika ce kuma jajirtacciya mai neman na kanta, ta yi jan hankali ga mata kan su yi biyayya ga mazajensu, su nemi halal, sannan su tsaya wuri guda domin kare mutuncinsu da na iyaye kai har ma da na ‘ya’yan da za su haifa. Haka nan ta shawarce su da su kiyaye yawace-yawace da yawan shige-shige marasa amfani.

Halima ta yi wannan jan hankali ne a tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM. Ga dai yadda ta kasance a tsakaninsu:

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • Ya Kamata A Bar Sinawa Su Yanke Shawara Kan Al’amuran Kasar Sin

Da fari za mu so sanin cikekken sunanki da tarihinki?

Assalamu alaikum warahmatullah. Sunana Halima Kassim, an haife ni a Karamar Hukumar Hadejia Jihar Jigawa. Na yi makarantar firamare a ‘Abdulkadir Special Primary School Hadejia,’ daga nan kuma bayan na gama na tafi Women Teachers College Malammadori, na yi J S S 1,2,3 daga nan na tafi Science Secondary School Jahun na yi S S S 1,2,3.na gama karatuna na secondary.

Shin Hajiya Halima matar aure ce ko kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Eh to a yanzu dai ba ni da aure bayan na gama sikandire na yi aure ina tare da mijina cikin jin dadi da kwanciyar hankali ya amsa kiran Ubangijinsa wato Allah ya yi masa rasuwa sakamako hatsarin mota an tura shi aiki a hanyarsa ta tafiya.

Shin kun haihu da shi kafin ya rasu ko kuma baku haihu ba?

Eh Allah ya azirta mu da da daya.

Bayan rasuwarsa ba ki sake wani auren ba?

Bayan na gama takaba sai na koma karatu na yi Diploma a Enbironment Menegment, sannan kuma da na samu kamar shekaru uku a tsakani na sake komawa makaranta na yi National Diploma For History yanzu kuma ina H .N.D. na kusa gamawa.

To Hajiya Halima idan kin gama HND za ki ci gaba ne da karatu ko kuma za ki yi aure?

Eh, duk wanda ya samu zan yi in sha Allahu in aure ne muna fatan Allah ya kawo miji nigari.

Hajiya Halima, duk karatun nan da kike yi kina aiki ne ko kuma karatun ne kike ta yi?

Eh to da lokacin ina gidan mijina na samu aiki ina dan yi a Local Gobernment, to tun da Allah yai masa rasuwa na dawo gidammu kara tun dai nake yi sai dai kuma ina taba kasuwanci haka.

Me kasuwanci naki ya kunsa?

Ina sayar da kamar akwai keken dinki da turaren wuta takalma da kayayyaki haka.

Mene ne ya ja hankalin ki kika fada kasuwanci, bayan ga karatu da kike yi?

To neman kudi ai ya zama dole a wannan rayuwar tamu ba sai ka je kana karamar murya kana ruko ba idan kana dan kasuwancin ka za ka rufa wa kanka asiri har ka taimaki wani ma, sannan za ka iya daukar dawainiyar kanka ba za ka nemi kudi a hannunka ka rasa ba, sannan a wajen karatumma za ka samu ciniki sosai to kin ga ka hada abu biyu kenan za ka ci riba biyu.

A zamanki na aure shin kin taba fuskatar wani kalubale kin san rayuwar zaman aure sai hakuri kafin maigida ya rasu?

Eh to ai ba za ka ce komai ba ita dama rayuwa zo mu zauna zo mu saba ce amma dai ni tsakani na da shi babu wani abu da ya taba shiga tsakanina da shi wanda za a ce wai gashi har an shiga tsakaninmu ko kuma wai gida su ji zama muke na nutsu da kwanciyar hankali saboda mutum ne mai kirki da gaskiya da rikon amana babu macen da za ta ce ta same shi a matsayin miji baji dadin zama da shi ba fatana shi ne Allah ya jikan sa da rahma.

To a harkar kasuwanci ki fa ba ki taba samun wani kalubale ba?

Kana kasuwanci ai ba za ka ce baka samu kalubale ba saboda akwai harkar bashi wani zai dau kayanka kafin ya ba ka kudin sai ya wahalar da kai, wani kuma sai ranka ya baci wani ba zai baka kudin ba haka zaka hakura ka barshi, dama haka kasuwanci ya kunsa akwai riba akwai kuma rashin riba sannan akwai faduwa akwai asara sai na ce ni kam Alhamdulillah.

Zuwa yanzu wace irin nasara kika samu a kasuwancinki?

To Alhamdulillah, gaskiya na samu nasarori dama gaskiya ina iya daukar kaina da har ma na taimakawa wani to kinga sai dai na ce Alhamdulillah nasarori na same su da yawa ba zan ma iya kirga su ba gaskiya sai godiya.

Wanne irin addu,a ne idan akayi miki kike jin dadi?

Addu’a duk addu’a ce, kuma duk addu’ar da aka yi maka za ka ji dadi mana har ma a ce Allah yai maka albarka da zuri’a baki daya.

Ada can kafin yanzu mene ne burinki?

A gaskiya ina da burin zama likita na yi ta kokarin hakan amma kin san kana naka Allah yana nasa kuma na Allah shi ne daidai Allah ya sa haka shi ya fi zama alkhairi.

Ga karatu ga kasuwanci ga kuma kula da danki da kika ce an bar miki, ta ya ya kike gudanar da hutunki?

Kasuwanci ai baya hana hutu, sannan kuma karatu ma shi ma idan an yi hutu zan samu na huta, daya kuma ba zai hana ni hutu ba.

Wane irin kwarin kwiwa kike samu a wajen iyaye a kan harkar karatunki da kuma kasuwanci ki?

Alhamdulillah ina samun kwarin kwiwa sosai a wajen iyaye tun suna da rai shi ya sa bayan sun rasu ma ban gajiya ba daga kasuwanci har karatu.

Kawaye fa?

To ni dai gaskiya bani da wata takamaimiyar kawa saboda mu gidammu ba,a fita daga makaranta sai gida sannan mu a tsarin gidammu mun saba da kulle, saboda mu gidammu ko aikin ka aka yi babammu yana kofar gida zai tambaye ka ina za ka idan ka ce aikenka aka yi zai ce ka koma gida a aiki namiji to shi ya sa to shi ya sa ma za ki ga bamu da kawaye.

A karshe wacce irin shawara za ki ba ‘yan ‘uwanki mata?

Shawarar da zan ba wa ‘yan uwana mata duk inda ‘ya mace take ta tsare kanta, sannan kuma ta kiyaye duk wani abubuwa da zai jawo mata matsala a rayuwar ta, ta ji tsoron Allah kuma ta kare kanta da mutunci ta da mutuncin iyayenta ta yi wa kanta mutunci ta bar yawaceyawace da shige-shige, sannan kuma mutum ya tsaya a waje daya ya kama sana’a kar ka ce za ka dogara da wani saboda dogaro da wani ba abu ne tabbatacce ba saboda Allah kadai ne za ka dogara da shi mutum idan ka dogara da wata ran akwai gajiyawa.

Wannan ita ce shawarar da zan ba wa ‘yan’uwana mata, sannan kuma a yi zaman aure a bi miji sau da kafa saboda aljannarki tana karkashi kafar mijinki .

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa (3)

Kananan Sana’oi Da Ci Gaban Kasa (3)

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.