Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Matar Gwamnan Bauchi Ta Bukaci Iyaye Mata Su Kara Azama Kan Tarbiyyantarwa

by Khalid Idris Doya
November 24, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Matar Gwamnan Bauchi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Uwar gidan gwamnan Jihar Bauchi Hajiya Aisha Bala Abdulkadir Muhammad ta bayyana cewa mata su na taka muhimmiyar rawa da ginshikin samar da shugabanci na gari, idan aka yi la’akari da hidimar tarbiyan al’umma.

Ta fadi hakan ne a wajen wata bita na kwana biyu 2 da ofishinta ya shirya wa matan Kwamishinoni da matan shugabbanin kananan hukomomi, tare da hadin gwiwan wata kungiya mai zaman kanta (Synistania Nigeria Limited) wanda ya gudana a dakin taro na gidan gwamnati.

samndaads

Aisha Bala ta jaddada cewa matan shugabanni a matakai daban-daban su na da jan aiki ta wajen fadakarwa da nusar da al’umma musamman matasa kan shugabancin da ake masu, na gari ko akasin hakan.

Bugu da kari ta kira yi mata da su ci gaba da aiwatar da ayyukansu na jinkai da tausayawa, kana ta ce sun yi amfani da abubuwan da aka gaya masu a yayin bitar, in sun koma cikin al’ummar da suke shugabanta, hakan zai bai wa gwamnati samun nasara a gudanar da shugabancin mutane.

A nashi jawabin maraba, Kwamishinan kananan hukomomi da masarautun gargajiya Alhaji Abdurrazak Nuhu Zaki, ya yaba wa uwar gidan gwamnan kan irin ayyukkan ta na jinkai da kuma shirya irin wannan taro na karin ilimi.

Ya ce “Ki na cire wa mata kitse a wuta ta wajen wayar masu da kai, ina jan hankalin wadanda aka shirya taron domin su, da su yi amfani da damar da suka samu, kar su rika dinki ana warwarewa, ku rika koyi da irin ayyukan da Uwar gidan gwamnan ta ke yi, da kuma dogaro da kai, don tabbatar da shugabanci na gari.”

Har-ila-yau, shugaban hukumar kula da marayu da marasa galihu jihar Bauchi, Misis Hassana Arkila ta ce wannan bitar ya zo a daidai, kuma ta ce sai an hada karfi da karfe kafin a samu nasarar abun da gwamnati ta sa gaba akai, ta kara da cewa dole ne a sake sabon lale ta wajen tarbiyyar yara musamman a arewacin Nijeriya.

“Ba za mu zura ido yaranmu su na lalacewa ba, da shaye shaye da sara suka, da fyade da fashi da makami, dukkan mu muna da aiki tukuru a gabanmu kan tarbiyyar ‘ya’yan mu baki daya,” ta ce.

A wajen taron da ya daga cikin kasidar da Dakta Musa Adamu Wunti, na Jami’ar Jihar Bauchi dake Gadau, ya gabatar da takarda inda ta yi nuni da cewa, “Mata su na da kaso mai tsoka ta wajen gina al’umma, da kuma shugabanci na gari, bin doka da oda da zimman ayyukan da za su kawo ci gaba, da zaman lafiyan jama’a bakidaya.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Shekaru 63: Jonathan Ya Gode Wa Gwamnan Bauchi Da Sauran Gwamnoni

Next Post

Sarkin Samarin Nijeriya Ya Ziyarci Hausawa Mazauna Legas

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Khalid Idris Doya
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post
Hausawa Mazauna Legas

Sarkin Samarin Nijeriya Ya Ziyarci Hausawa Mazauna Legas

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version