ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Mata Ke Shiga Sakamakon Rashin Samun Gamsuwa Daga Mazajensu

by Sani Anwar
2 years ago
Mata

Akwai mata da dama masu fuskantar matsaloli na rashin samun gamsuwar jima’i daga wajen mazajensu a wannan zamani da ba su iya fada musu, wanda hakan ke kara jefa su cikin damuwa.

Wasu matan na tsintar kansu wajen bin mazajen banza a waje, sakamakon rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wurin mazajen nasu, duk da dai bai kamata wannan ya zama hujja ta yin masha’a ba.

Ya kamata a lura da cewa, duk irin jaraba ko karfin sha’awar da mace ke da ita; idan har namiji na iya gamsar da ita yadda ya kamata, ba za ta taba daga kai ta kalli wani namijin daban ba.

ADVERTISEMENT

Amma shi kuwa namiji, duk yadda kika kai da iya gamsar da shi ko sanya shi nishadi; da zarar ya hango wata daban kuma sai dai kawai wanda Allah ya tsare. Har ila yau, matsalar da ke faruwa a wannan lokaci; musamman ganin yadda matan aure ke bin maza a waje, ya samo asali ne daga wadannan abubuwa da za a zayyano kamar haka:

1- Rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wajen namiji, in har mace za ta ci ta sha ta koshi, sannan hankalinta a kwance; ai kuwa wajibi ne ta bukaci da namiji a kusa da ita.
Hakika bincike ya tabbatar da cewa, ‘ya’ya mata sun fi maza karfin sha’awa, domin kuwa idan har mace na da lafiya; dole ne ta bukaci namiji, sannan ba kowace mace ce ke iya mallakar kanta ba; musamman idan bukatar da namiji ta bijiro mata, shi yasa wasu suke kai wa ga fadawa ga halaka.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Amma, mafi yawan lokuta idan muka duba; za mu tarar da cewa laifin mazan ne; domin kuwa idan har namiji zai biya wa matarsa bukata, ko kadan ba za ta taba kallon wani namijin daban ba.

Mene ne ke hana wasu matan samun gamsuwa daga mazajensu?

– Rashin cikakkiyar lafiya daga wajen da namiji, kamar matsalar sanyi, basir, hawan jini, ciwon siga, rashin abinci mai gina jiki ko matsalar istimna’i da sauran cututtuka da ka iya taba lafiyar al’aurar da namiji.

– Tana iya yiwuwa kuma matsalar daga wajen macen ne, kamar matsalar da suke fama da ita ta sanyi (infection), wanda ke hana su samun gamsuwa ko jin dadin saduwa da miji ko kuma matsalar iska, wato namijin dare (Aljanin da yake aurar mace), sai ya hana ta jin dadin saduwa da mijinta kwata-kwata.

2- Rashin kwarewa wajen tarawa da matarka tare kuma da rashin cikakken ilimin yadda za ka sarrafa ta, ta yadda za ta samu gamsuwa tare da nishadi daga wurinka.

3- Son kai daga bangaren da namiji: kusan kaso 9 cikin 10 na maza, na da matukar son kawunansu ta wajen biya wa kansu bukatar aure. Domin kuwa, da zarar tasu bukatar ta biya; babu ruwansu kuma da bukatar ‘ya mace.

Saboda haka, ya zama wajibi mu kula da matanmu tare da kokarin sauke nauyinsu da ke kanmu, domin tseratar da su daga fada wa irin wannan mummunan hali ko halaka, wato bin wasu mazajen a waje.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.