• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Mata Ke Shiga Sakamakon Rashin Samun Gamsuwa Daga Mazajensu

by Sani Anwar
1 year ago
in Kiwon Lafiya
0
Halin Da Mata Ke Shiga Sakamakon Rashin Samun Gamsuwa Daga Mazajensu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai mata da dama masu fuskantar matsaloli na rashin samun gamsuwar jima’i daga wajen mazajensu a wannan zamani da ba su iya fada musu, wanda hakan ke kara jefa su cikin damuwa.

Wasu matan na tsintar kansu wajen bin mazajen banza a waje, sakamakon rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wurin mazajen nasu, duk da dai bai kamata wannan ya zama hujja ta yin masha’a ba.

Ya kamata a lura da cewa, duk irin jaraba ko karfin sha’awar da mace ke da ita; idan har namiji na iya gamsar da ita yadda ya kamata, ba za ta taba daga kai ta kalli wani namijin daban ba.

Amma shi kuwa namiji, duk yadda kika kai da iya gamsar da shi ko sanya shi nishadi; da zarar ya hango wata daban kuma sai dai kawai wanda Allah ya tsare. Har ila yau, matsalar da ke faruwa a wannan lokaci; musamman ganin yadda matan aure ke bin maza a waje, ya samo asali ne daga wadannan abubuwa da za a zayyano kamar haka:

1- Rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wajen namiji, in har mace za ta ci ta sha ta koshi, sannan hankalinta a kwance; ai kuwa wajibi ne ta bukaci da namiji a kusa da ita.
Hakika bincike ya tabbatar da cewa, ‘ya’ya mata sun fi maza karfin sha’awa, domin kuwa idan har mace na da lafiya; dole ne ta bukaci namiji, sannan ba kowace mace ce ke iya mallakar kanta ba; musamman idan bukatar da namiji ta bijiro mata, shi yasa wasu suke kai wa ga fadawa ga halaka.

Labarai Masu Nasaba

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Amma, mafi yawan lokuta idan muka duba; za mu tarar da cewa laifin mazan ne; domin kuwa idan har namiji zai biya wa matarsa bukata, ko kadan ba za ta taba kallon wani namijin daban ba.

Mene ne ke hana wasu matan samun gamsuwa daga mazajensu?

– Rashin cikakkiyar lafiya daga wajen da namiji, kamar matsalar sanyi, basir, hawan jini, ciwon siga, rashin abinci mai gina jiki ko matsalar istimna’i da sauran cututtuka da ka iya taba lafiyar al’aurar da namiji.

– Tana iya yiwuwa kuma matsalar daga wajen macen ne, kamar matsalar da suke fama da ita ta sanyi (infection), wanda ke hana su samun gamsuwa ko jin dadin saduwa da miji ko kuma matsalar iska, wato namijin dare (Aljanin da yake aurar mace), sai ya hana ta jin dadin saduwa da mijinta kwata-kwata.

2- Rashin kwarewa wajen tarawa da matarka tare kuma da rashin cikakken ilimin yadda za ka sarrafa ta, ta yadda za ta samu gamsuwa tare da nishadi daga wurinka.

3- Son kai daga bangaren da namiji: kusan kaso 9 cikin 10 na maza, na da matukar son kawunansu ta wajen biya wa kansu bukatar aure. Domin kuwa, da zarar tasu bukatar ta biya; babu ruwansu kuma da bukatar ‘ya mace.

Saboda haka, ya zama wajibi mu kula da matanmu tare da kokarin sauke nauyinsu da ke kanmu, domin tseratar da su daga fada wa irin wannan mummunan hali ko halaka, wato bin wasu mazajen a waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karancin saduwa a aureRayuwar aureYawon ta zubar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Kama Hanyar Zuwa Faransa Da Serbia Da Hungary Domin Ziyarar Aiki

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

Related

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
Kiwon Lafiya

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

3 days ago
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

5 days ago
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 
Kiwon Lafiya

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

1 week ago
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
Kiwon Lafiya

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

3 weeks ago
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

4 weeks ago
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa
Kiwon Lafiya

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

1 month ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.