ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Mata Ke Shiga Sakamakon Rashin Samun Gamsuwa Daga Mazajensu

by Sani Anwar
2 years ago
Mata

Akwai mata da dama masu fuskantar matsaloli na rashin samun gamsuwar jima’i daga wajen mazajensu a wannan zamani da ba su iya fada musu, wanda hakan ke kara jefa su cikin damuwa.

Wasu matan na tsintar kansu wajen bin mazajen banza a waje, sakamakon rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wurin mazajen nasu, duk da dai bai kamata wannan ya zama hujja ta yin masha’a ba.

Ya kamata a lura da cewa, duk irin jaraba ko karfin sha’awar da mace ke da ita; idan har namiji na iya gamsar da ita yadda ya kamata, ba za ta taba daga kai ta kalli wani namijin daban ba.

ADVERTISEMENT

Amma shi kuwa namiji, duk yadda kika kai da iya gamsar da shi ko sanya shi nishadi; da zarar ya hango wata daban kuma sai dai kawai wanda Allah ya tsare. Har ila yau, matsalar da ke faruwa a wannan lokaci; musamman ganin yadda matan aure ke bin maza a waje, ya samo asali ne daga wadannan abubuwa da za a zayyano kamar haka:

1- Rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wajen namiji, in har mace za ta ci ta sha ta koshi, sannan hankalinta a kwance; ai kuwa wajibi ne ta bukaci da namiji a kusa da ita.
Hakika bincike ya tabbatar da cewa, ‘ya’ya mata sun fi maza karfin sha’awa, domin kuwa idan har mace na da lafiya; dole ne ta bukaci namiji, sannan ba kowace mace ce ke iya mallakar kanta ba; musamman idan bukatar da namiji ta bijiro mata, shi yasa wasu suke kai wa ga fadawa ga halaka.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Amma, mafi yawan lokuta idan muka duba; za mu tarar da cewa laifin mazan ne; domin kuwa idan har namiji zai biya wa matarsa bukata, ko kadan ba za ta taba kallon wani namijin daban ba.

Mene ne ke hana wasu matan samun gamsuwa daga mazajensu?

– Rashin cikakkiyar lafiya daga wajen da namiji, kamar matsalar sanyi, basir, hawan jini, ciwon siga, rashin abinci mai gina jiki ko matsalar istimna’i da sauran cututtuka da ka iya taba lafiyar al’aurar da namiji.

– Tana iya yiwuwa kuma matsalar daga wajen macen ne, kamar matsalar da suke fama da ita ta sanyi (infection), wanda ke hana su samun gamsuwa ko jin dadin saduwa da miji ko kuma matsalar iska, wato namijin dare (Aljanin da yake aurar mace), sai ya hana ta jin dadin saduwa da mijinta kwata-kwata.

2- Rashin kwarewa wajen tarawa da matarka tare kuma da rashin cikakken ilimin yadda za ka sarrafa ta, ta yadda za ta samu gamsuwa tare da nishadi daga wurinka.

3- Son kai daga bangaren da namiji: kusan kaso 9 cikin 10 na maza, na da matukar son kawunansu ta wajen biya wa kansu bukatar aure. Domin kuwa, da zarar tasu bukatar ta biya; babu ruwansu kuma da bukatar ‘ya mace.

Saboda haka, ya zama wajibi mu kula da matanmu tare da kokarin sauke nauyinsu da ke kanmu, domin tseratar da su daga fada wa irin wannan mummunan hali ko halaka, wato bin wasu mazajen a waje.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.