ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Mata Ke Shiga Sakamakon Rashin Samun Gamsuwa Daga Mazajensu

by Sani Anwar
2 years ago
Mata

Akwai mata da dama masu fuskantar matsaloli na rashin samun gamsuwar jima’i daga wajen mazajensu a wannan zamani da ba su iya fada musu, wanda hakan ke kara jefa su cikin damuwa.

Wasu matan na tsintar kansu wajen bin mazajen banza a waje, sakamakon rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wurin mazajen nasu, duk da dai bai kamata wannan ya zama hujja ta yin masha’a ba.

Ya kamata a lura da cewa, duk irin jaraba ko karfin sha’awar da mace ke da ita; idan har namiji na iya gamsar da ita yadda ya kamata, ba za ta taba daga kai ta kalli wani namijin daban ba.

ADVERTISEMENT

Amma shi kuwa namiji, duk yadda kika kai da iya gamsar da shi ko sanya shi nishadi; da zarar ya hango wata daban kuma sai dai kawai wanda Allah ya tsare. Har ila yau, matsalar da ke faruwa a wannan lokaci; musamman ganin yadda matan aure ke bin maza a waje, ya samo asali ne daga wadannan abubuwa da za a zayyano kamar haka:

1- Rashin samun cikakkiyar gamsuwa daga wajen namiji, in har mace za ta ci ta sha ta koshi, sannan hankalinta a kwance; ai kuwa wajibi ne ta bukaci da namiji a kusa da ita.
Hakika bincike ya tabbatar da cewa, ‘ya’ya mata sun fi maza karfin sha’awa, domin kuwa idan har mace na da lafiya; dole ne ta bukaci namiji, sannan ba kowace mace ce ke iya mallakar kanta ba; musamman idan bukatar da namiji ta bijiro mata, shi yasa wasu suke kai wa ga fadawa ga halaka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

Amma, mafi yawan lokuta idan muka duba; za mu tarar da cewa laifin mazan ne; domin kuwa idan har namiji zai biya wa matarsa bukata, ko kadan ba za ta taba kallon wani namijin daban ba.

Mene ne ke hana wasu matan samun gamsuwa daga mazajensu?

– Rashin cikakkiyar lafiya daga wajen da namiji, kamar matsalar sanyi, basir, hawan jini, ciwon siga, rashin abinci mai gina jiki ko matsalar istimna’i da sauran cututtuka da ka iya taba lafiyar al’aurar da namiji.

– Tana iya yiwuwa kuma matsalar daga wajen macen ne, kamar matsalar da suke fama da ita ta sanyi (infection), wanda ke hana su samun gamsuwa ko jin dadin saduwa da miji ko kuma matsalar iska, wato namijin dare (Aljanin da yake aurar mace), sai ya hana ta jin dadin saduwa da mijinta kwata-kwata.

2- Rashin kwarewa wajen tarawa da matarka tare kuma da rashin cikakken ilimin yadda za ka sarrafa ta, ta yadda za ta samu gamsuwa tare da nishadi daga wurinka.

3- Son kai daga bangaren da namiji: kusan kaso 9 cikin 10 na maza, na da matukar son kawunansu ta wajen biya wa kansu bukatar aure. Domin kuwa, da zarar tasu bukatar ta biya; babu ruwansu kuma da bukatar ‘ya mace.

Saboda haka, ya zama wajibi mu kula da matanmu tare da kokarin sauke nauyinsu da ke kanmu, domin tseratar da su daga fada wa irin wannan mummunan hali ko halaka, wato bin wasu mazajen a waje.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
Manyan Labarai

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

September 3, 2026
Mata
Kiwon Lafiya

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

August 30, 2026
Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
Kiwon Lafiya

Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?

August 29, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Bayan Isa Kasar Faransa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.