• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Rayuwa

Masana harkokin kudi da na tattalin arziki sun bayyana wa Shugaban kasa Bola Tinubu cewa karuwar kaso 3.19 na kudin shigar Nijeriya a zango na biyu na 2024 ya gaza fito da hakikanin halin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar kiddiga ta Nijeriya (NBS) ta sanar a ranar Litinin cewa kudin shigan Nijeriya ya karu da kaso 3.19 cikin 100 a zango na biyu na shekarar 2024, wanda ya dara da kaso 2.98 cikin 100 a zangon farko.

  • Kamfanin Abinci Na BUA Ya Samu Ribar Naira Biliyan 130 A Wata Shida Na 2024
  • Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

A cewar rahoton NBS, bangaren kamfanoni da ayyuka sun ba da gagarumin gudunmawa wajen ci gaban kudin shigan a zango na biyun.

Bangaren ayyukan yau da kullum ya ba da kaso 58.76 na kudaden shiga, inda bangarorin da ba na mai ba suka kawo kaso 94.30, yayin da kuma bangaren mai ya kawo kaso 5.70 a zango na biyun.

Duk da wannan ci gaban da kudin shigan kasan ya samu, masana tattalin arziki sun yi tambayar mene ne ya sanya har yanzu talakawan Nijeriya ba su ga tasirin karin da aka samu ba.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Bugu da kari, farashin kayayyaki na nan a kan tsadarsu duk da tsare-tsaren da Tinubu ya bijiro da su.

Wani masani kan tattalin arziki, Farfesa Segun Ajibola, tsohon shugaban kungiyar kwararru a bangaren banki, ya ce, ci gaban bai taba rayuwar talakawa ba ko kawo sauyi daga halin da suke ciki.

Ya nemi gwamnati da ta bullo da hanyoyin da suka dace da talaka zai samu sauki da ganin tasirin ci gaban da ake samu na kai tsaye.

A cewarsa, ci gaban ya kamata ne ya shiga cikin abubuwan da suke na bukatun jama’a na farko-farko wato irin kayan abinci kafin a je ga manyan bangarori na ayyukan yau da gobe, wanda in aka samu hakan talaka zai shaida.

Shi ma masanin hada-hadar kudade, Gbolade Idakolo, ya ce, karuwar kudin shigan bai janyo sauyi kan lamarin tattalin arziki daga tushe a wajen talaka ba.

Don haka ne ya ce a yi la’akari da hakikanin halin da ake ciki ta yadda za a nemi tunkarar abubuwan da suke akwai domin samun sauyi mai ma’ana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Zaben Kananan Hukumomin Kano: 'Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.