• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

by Khalid Idris Doya
9 months ago
in Tattalin Arziki
0
Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin kudi da na tattalin arziki sun bayyana wa Shugaban kasa Bola Tinubu cewa karuwar kaso 3.19 na kudin shigar Nijeriya a zango na biyu na 2024 ya gaza fito da hakikanin halin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar kiddiga ta Nijeriya (NBS) ta sanar a ranar Litinin cewa kudin shigan Nijeriya ya karu da kaso 3.19 cikin 100 a zango na biyu na shekarar 2024, wanda ya dara da kaso 2.98 cikin 100 a zangon farko.

  • Kamfanin Abinci Na BUA Ya Samu Ribar Naira Biliyan 130 A Wata Shida Na 2024
  • Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

A cewar rahoton NBS, bangaren kamfanoni da ayyuka sun ba da gagarumin gudunmawa wajen ci gaban kudin shigan a zango na biyun.

Bangaren ayyukan yau da kullum ya ba da kaso 58.76 na kudaden shiga, inda bangarorin da ba na mai ba suka kawo kaso 94.30, yayin da kuma bangaren mai ya kawo kaso 5.70 a zango na biyun.

Duk da wannan ci gaban da kudin shigan kasan ya samu, masana tattalin arziki sun yi tambayar mene ne ya sanya har yanzu talakawan Nijeriya ba su ga tasirin karin da aka samu ba.

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Bugu da kari, farashin kayayyaki na nan a kan tsadarsu duk da tsare-tsaren da Tinubu ya bijiro da su.

Wani masani kan tattalin arziki, Farfesa Segun Ajibola, tsohon shugaban kungiyar kwararru a bangaren banki, ya ce, ci gaban bai taba rayuwar talakawa ba ko kawo sauyi daga halin da suke ciki.

Ya nemi gwamnati da ta bullo da hanyoyin da suka dace da talaka zai samu sauki da ganin tasirin ci gaban da ake samu na kai tsaye.

A cewarsa, ci gaban ya kamata ne ya shiga cikin abubuwan da suke na bukatun jama’a na farko-farko wato irin kayan abinci kafin a je ga manyan bangarori na ayyukan yau da gobe, wanda in aka samu hakan talaka zai shaida.

Shi ma masanin hada-hadar kudade, Gbolade Idakolo, ya ce, karuwar kudin shigan bai janyo sauyi kan lamarin tattalin arziki daga tushe a wajen talaka ba.

Don haka ne ya ce a yi la’akari da hakikanin halin da ake ciki ta yadda za a nemi tunkarar abubuwan da suke akwai domin samun sauyi mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KudiMoneyTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Ziyarci Yankunan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Gummi

Next Post

Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

7 days ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

Zaben Kananan Hukumomin Kano: 'Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.