• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum 6,900 da ake zargin mayakan Boko Haram ne kuma a halin yanzu za su fuskanci shari’a ta wucin gadi, a cewar gwamnatin Jihar Borno.

Kwamishiniyar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jihar, Zuwaira Gambo ce ta bayyana hakan a lokacin da ake kammala wani shiri na yada al’ada da koyo da Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin Foundation ta shirya a Maiduguri Babban Birnin Jihar Borno a ranar Talata.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

A cewarta, kusan mutum 9,000 ne suka koma cikin al’umma, kuma shirin ya samu gagarumar nasara.

“Ya zuwa yanzu, kimanin ‘yan ta’addan Boko Haram 200,000 da iyalansu sun mika wuya ga gwamnatin jihar.

“Bari na fayyace, muna da mayakan Boko Haram na gaskiya kusan 6,900 a hannunmu, kuma za su fuskanci shari’ar wucin gadi saboda sun aikata laifuka. Muna aiki akan cewa; mayakan ne na gaske,” in ji ta.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Adalci kwarya wata hanya ce ta samar da zaman lafiya da ke neman magance abubuwan da suka gada na munanan laifuka da kuma kawo karshen tashe-tashen hankula da ke faruwa a lokuta daban-daban, ciki har da ramawa, sulhu, gurfanar da su a gaban kotu, da yin afuwa.

Babbar Darakta ta Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin, Hamsatu Allamin, ta bayyana cewa mutanen da suka mika wuya sun yi nadamar alakarsu da Boko Haram.

A cewarta, sun bayyana nadamar kasancewarsu a cikin kungiyar ta’addancin, saboda rashin ilimi da kuma saukin yadda ‘yan tada kayar baya suka yi garkuwa da su.

“Idan ’yan Boko Haram sun yi amfani da akidarsu ta addini wajen wanke wa mutane kwakwalwa su shiga cikin su, mu ma mu yi amfani da addini mu fada musu gaskiya. Don haka, ina ba da shawarar cewa gwamnati ta yi amfani da addini don gyara wannan labari mai tayar da hankali,” in ji ta.

A karkashin shirin ‘Ginin sulhu: Hanyar da ta dace da al’umma don kawar da mata da ‘yan mata a Jihar Borno,’ an wayar da kan mata sama da 800 da aka zalunta kuma yanzu suna ba da gudummawa ga al’umma.

Ta kara da cewa “Sun shirya rungumar sabuwar rayuwa wacce ba ta da tashe-tashen hankula kuma su zama masu rike da madafun iko a cikin al’umma, tare da ba da gudummawa ga samar da zaman lafiya da ci gaban al’ummominsu baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramKotuMayaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa Shida Da Suka Kamata A Sani Game Da Bishiyar Kanya

Next Post

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.