• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutum 6,900 da ake zargin mayakan Boko Haram ne kuma a halin yanzu za su fuskanci shari’a ta wucin gadi, a cewar gwamnatin Jihar Borno.

Kwamishiniyar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jihar, Zuwaira Gambo ce ta bayyana hakan a lokacin da ake kammala wani shiri na yada al’ada da koyo da Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin Foundation ta shirya a Maiduguri Babban Birnin Jihar Borno a ranar Talata.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

A cewarta, kusan mutum 9,000 ne suka koma cikin al’umma, kuma shirin ya samu gagarumar nasara.

“Ya zuwa yanzu, kimanin ‘yan ta’addan Boko Haram 200,000 da iyalansu sun mika wuya ga gwamnatin jihar.

“Bari na fayyace, muna da mayakan Boko Haram na gaskiya kusan 6,900 a hannunmu, kuma za su fuskanci shari’ar wucin gadi saboda sun aikata laifuka. Muna aiki akan cewa; mayakan ne na gaske,” in ji ta.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Adalci kwarya wata hanya ce ta samar da zaman lafiya da ke neman magance abubuwan da suka gada na munanan laifuka da kuma kawo karshen tashe-tashen hankula da ke faruwa a lokuta daban-daban, ciki har da ramawa, sulhu, gurfanar da su a gaban kotu, da yin afuwa.

Babbar Darakta ta Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin, Hamsatu Allamin, ta bayyana cewa mutanen da suka mika wuya sun yi nadamar alakarsu da Boko Haram.

A cewarta, sun bayyana nadamar kasancewarsu a cikin kungiyar ta’addancin, saboda rashin ilimi da kuma saukin yadda ‘yan tada kayar baya suka yi garkuwa da su.

“Idan ’yan Boko Haram sun yi amfani da akidarsu ta addini wajen wanke wa mutane kwakwalwa su shiga cikin su, mu ma mu yi amfani da addini mu fada musu gaskiya. Don haka, ina ba da shawarar cewa gwamnati ta yi amfani da addini don gyara wannan labari mai tayar da hankali,” in ji ta.

A karkashin shirin ‘Ginin sulhu: Hanyar da ta dace da al’umma don kawar da mata da ‘yan mata a Jihar Borno,’ an wayar da kan mata sama da 800 da aka zalunta kuma yanzu suna ba da gudummawa ga al’umma.

Ta kara da cewa “Sun shirya rungumar sabuwar rayuwa wacce ba ta da tashe-tashen hankula kuma su zama masu rike da madafun iko a cikin al’umma, tare da ba da gudummawa ga samar da zaman lafiya da ci gaban al’ummominsu baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramKotuMayaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa Shida Da Suka Kamata A Sani Game Da Bishiyar Kanya

Next Post

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

7 days ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

7 days ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

2 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
Next Post
Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.