ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Haram

Akalla mutum 6,900 da ake zargin mayakan Boko Haram ne kuma a halin yanzu za su fuskanci shari’a ta wucin gadi, a cewar gwamnatin Jihar Borno.

Kwamishiniyar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jihar, Zuwaira Gambo ce ta bayyana hakan a lokacin da ake kammala wani shiri na yada al’ada da koyo da Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin Foundation ta shirya a Maiduguri Babban Birnin Jihar Borno a ranar Talata.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

A cewarta, kusan mutum 9,000 ne suka koma cikin al’umma, kuma shirin ya samu gagarumar nasara.

ADVERTISEMENT

“Ya zuwa yanzu, kimanin ‘yan ta’addan Boko Haram 200,000 da iyalansu sun mika wuya ga gwamnatin jihar.

“Bari na fayyace, muna da mayakan Boko Haram na gaskiya kusan 6,900 a hannunmu, kuma za su fuskanci shari’ar wucin gadi saboda sun aikata laifuka. Muna aiki akan cewa; mayakan ne na gaske,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Adalci kwarya wata hanya ce ta samar da zaman lafiya da ke neman magance abubuwan da suka gada na munanan laifuka da kuma kawo karshen tashe-tashen hankula da ke faruwa a lokuta daban-daban, ciki har da ramawa, sulhu, gurfanar da su a gaban kotu, da yin afuwa.

Babbar Darakta ta Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin, Hamsatu Allamin, ta bayyana cewa mutanen da suka mika wuya sun yi nadamar alakarsu da Boko Haram.

A cewarta, sun bayyana nadamar kasancewarsu a cikin kungiyar ta’addancin, saboda rashin ilimi da kuma saukin yadda ‘yan tada kayar baya suka yi garkuwa da su.

“Idan ’yan Boko Haram sun yi amfani da akidarsu ta addini wajen wanke wa mutane kwakwalwa su shiga cikin su, mu ma mu yi amfani da addini mu fada musu gaskiya. Don haka, ina ba da shawarar cewa gwamnati ta yi amfani da addini don gyara wannan labari mai tayar da hankali,” in ji ta.

A karkashin shirin ‘Ginin sulhu: Hanyar da ta dace da al’umma don kawar da mata da ‘yan mata a Jihar Borno,’ an wayar da kan mata sama da 800 da aka zalunta kuma yanzu suna ba da gudummawa ga al’umma.

Ta kara da cewa “Sun shirya rungumar sabuwar rayuwa wacce ba ta da tashe-tashen hankula kuma su zama masu rike da madafun iko a cikin al’umma, tare da ba da gudummawa ga samar da zaman lafiya da ci gaban al’ummominsu baki daya.”

Haram
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Lalata Kilo12,234 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 29, 2026
CBN

Majalisa Ta Yi Tsit Yayin Da Gwamnati Ke Keta Haddin Amso Bashi – Sarkin Sanusi II

June 29, 2026
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karin Agajin Gaggawa Na Yuan Miliyan 100 Ga Venezuela

June 29, 2026
Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

Labarin Lu Rongjie: Misalin Demokradiyya Da Shugabanci Mai Hidimtawa Al’umma

June 29, 2026
Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatun Biza Miliyan 1.34 Daga Hannun ’Yan Nijeriya

June 29, 2026
Yadda Yara Suka Kamo Harsasan Harbo Jirgin Sama A Yayin Kamun Kifi A Borno

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Da Philippines Na Keta Hakkoki Da Muradunta Na Teku

June 29, 2026
Xi Jinping Zai Bayar Da Lambar Yabo Ta Ranar 1 Ga Watan Yuli Tare Da Gabatar Da Jawabi Albarkacin Cikar JKS Shekaru 105 Da Kafuwa

Xi Jinping Zai Bayar Da Lambar Yabo Ta Ranar 1 Ga Watan Yuli Tare Da Gabatar Da Jawabi Albarkacin Cikar JKS Shekaru 105 Da Kafuwa

June 29, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Far Wa Makaranta, Sun Sace Ɗaliban NECO A Borno

Ƴan Ta’adda Sun Far Wa Makaranta, Sun Sace Ɗaliban NECO A Borno

June 29, 2026
Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

Gwamnan Kwara Ya Yi Tankaɗe Da Rairaye, Ya Kori Hadimansa

June 29, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.