ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan Boko Haram 6,900 Na Shirin Gurfana A Gaban Shari’a

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Haram

Akalla mutum 6,900 da ake zargin mayakan Boko Haram ne kuma a halin yanzu za su fuskanci shari’a ta wucin gadi, a cewar gwamnatin Jihar Borno.

Kwamishiniyar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jihar, Zuwaira Gambo ce ta bayyana hakan a lokacin da ake kammala wani shiri na yada al’ada da koyo da Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin Foundation ta shirya a Maiduguri Babban Birnin Jihar Borno a ranar Talata.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

A cewarta, kusan mutum 9,000 ne suka koma cikin al’umma, kuma shirin ya samu gagarumar nasara.

ADVERTISEMENT

“Ya zuwa yanzu, kimanin ‘yan ta’addan Boko Haram 200,000 da iyalansu sun mika wuya ga gwamnatin jihar.

“Bari na fayyace, muna da mayakan Boko Haram na gaskiya kusan 6,900 a hannunmu, kuma za su fuskanci shari’ar wucin gadi saboda sun aikata laifuka. Muna aiki akan cewa; mayakan ne na gaske,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Adalci kwarya wata hanya ce ta samar da zaman lafiya da ke neman magance abubuwan da suka gada na munanan laifuka da kuma kawo karshen tashe-tashen hankula da ke faruwa a lokuta daban-daban, ciki har da ramawa, sulhu, gurfanar da su a gaban kotu, da yin afuwa.

Babbar Darakta ta Gidauniyar Zaman Lafiya Da Ci Gaba ta Allamin, Hamsatu Allamin, ta bayyana cewa mutanen da suka mika wuya sun yi nadamar alakarsu da Boko Haram.

A cewarta, sun bayyana nadamar kasancewarsu a cikin kungiyar ta’addancin, saboda rashin ilimi da kuma saukin yadda ‘yan tada kayar baya suka yi garkuwa da su.

“Idan ’yan Boko Haram sun yi amfani da akidarsu ta addini wajen wanke wa mutane kwakwalwa su shiga cikin su, mu ma mu yi amfani da addini mu fada musu gaskiya. Don haka, ina ba da shawarar cewa gwamnati ta yi amfani da addini don gyara wannan labari mai tayar da hankali,” in ji ta.

A karkashin shirin ‘Ginin sulhu: Hanyar da ta dace da al’umma don kawar da mata da ‘yan mata a Jihar Borno,’ an wayar da kan mata sama da 800 da aka zalunta kuma yanzu suna ba da gudummawa ga al’umma.

Ta kara da cewa “Sun shirya rungumar sabuwar rayuwa wacce ba ta da tashe-tashen hankula kuma su zama masu rike da madafun iko a cikin al’umma, tare da ba da gudummawa ga samar da zaman lafiya da ci gaban al’ummominsu baki daya.”

Haram
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.