ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan ISWAP Da Boko Haram Sun Tafka Kazamin Fada A Tsakaninsu

by Sadiq
3 years ago
ISWAP

Rikicin da ya barke tsakanin bangaren mayakan Boko Haram da ISWAP, wanda aka ce an kashe ‘yan ta’adda da dama a cikin kwanaki ukun da suka gabata.

Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi, ya tattaro cewa fitaccen shugaban kungiyar Boko Haram, Ali Ngulde, a ranar 3 ga watan Disamba, ya jagoranci daruruwan mayaka dauke da muggan makamai daga tsaunin Mandara, inda suka kai farmaki kan sansanin ISWAP a wani gagarumin farmaki da suka kai musu.

  • An Fitar Da Rahoton Masana Kan Ra’ayin Kare Hakkin Dan Adam Na Sin
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Kwamishina A Binuwai Da Yin Awon-Gaba Da Wasu Mutum 3

Kazalika majiyoyin leken asiri sun shaida wa Makama cewa an fara arangama ne a sansanin Yuwe, wanda ya haifar da kazamin musayar wuta da mayakan Ngulde suka yi galaba a kan mayakan ISWAP tare da kashe 12 daga cikinsu sannan suka kwace makamansu.

ADVERTISEMENT

Ba da jimawa ba, majiyoyi sun ce mayakan na Boko Haram sun yi gaggawar tattara karin mayakan daga sansanin Abu Ikilima da ke Gaizuwa, Gabchari, Mantari da Mallum Masari.

A cewar kwararre na yaki da ‘yan ta’addan, an kashe mayakan ISWAP sama da 23 a ranar 4 ga watan Disamba, lokacin da bangaren Shekau na kungiyar Boko Haram suka rabu gida biyu, suka kai farmaki kan ISWAP a Ukuba, Arra da Sabil Huda.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Zagazola ya kara da cewa, a daren Lahadi, an ga wata tawagar mayakan da ke sansanin ISWAP a kusa da Kawuri da Aulari, inda a safiyar ranar Litinin wani babban shugaban ISWAP, Ba’ana Chingori, ya jagoranci wata tawagar mayakan da suka kai farmaki kan mayakan Boko Haram.

Rikicin da ya barke tsakanin bangarorin ‘yan ta’addar ya yi sanadiyar mutuwar mayaka da dama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD

Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa - MDD

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.