Dattawan Arewa sun bayyana cewa yankin ya rasa alkiblarsa sakamakon gazawar shugabanci da watsi da kyawawan ɗabi’u da suka gina yankin a baya.
Dattawan Sun yi wannan kira ne a taron tunawa da Marigayi Janar Hassan Usman Katsina da aka gudanar a gidan taro na Arewa House , Kaduna.
A jawabinsu, Shugaban taron Farfesa Ango Abdullahi, da Dakta Usman Bugaje da Manjo Hamza Al-Mustapha sun buƙaci shugabanni su rungumi gaskiya, riƙon amana da shugabanci nagari. Sun kuma ce farfaɗo da noma, inganta tsaro da amfani da albarkatun Arewa yadda ya kamata ne mafita ga matsalolin yankin.
Farfesa Ango Abdullahi, ya ce Arewa ta kauce wa kyawawan manufofi da dabi’un shugabanci na gaskiya, riƙon amana, da hidimar jama’a da magabatan yankin suka gada. Ya ce idan ba a dawo da waɗannan ƙimomi ba, matsalolin tsaro, talauci da koma bayan tattalin arziki za su ci gaba da ƙaruwa.
Dakta Usman Bugaje, ya ce yankin Arewa na fuskantar koma baya sakamakon taɓarɓarewar tsaro, ƙarancin samar da abinci da rashin ingantaccen shugabanci. Ya soki wasu daga cikin jagororin Arewa bisa yawan koke-koke ba tare da gabatar da mafita ba.
A nasa jawabin, Tsohon Dogarin Marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha, ya ce Arewa na fama da shugabanci marar alkibla da rashawa, yana mai kira ga shugabannin yankin da su gudanar da wani taron nazari na tsawon mako guda domin samar da ingantacciyar hanya ta ceto yankin.
Al-Mustapha ya ce Arewa na da dimbin albarkatun ƙasa da na ɗan’Adam, tare da bayyana cewa fannoni kamar basirar wucin gadi (AI), ma’adanai da albarkatun Tafkin Chadi na iya zama ginshiƙan bunƙasar tattalin arzikin yankin idan aka sarrafa su yadda ya kamata














