• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Bambancin Ra’ayi Na Kasar Sin Dangane Da Tsarin Kasa Da Kasa ?

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Mene Ne Bambancin Ra’ayi Na Kasar Sin Dangane Da Tsarin Kasa Da Kasa ?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin ziyarar Yusuf Maitama Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya, a kasar Sin a kwanan baya, wata maganar da ya fada ya burge ni, inda ya ce, “Yadda kasar Sin ke kallon tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na sauran kasashe: Ba ta kallon duniya a matsayin filin dambarwar siyasa, maimakon haka, tana neman karfafa hadewar yankuna da kasashe, ta shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.”

Wannan bambanci game da kasar Sin da minista Tuggar ya ambata ya samu tabbatuwa ta bakin mutanen sauran kasashe. Misali, Roger McKenzie, wani editan jaridar Morning Star ta kasar Birtaniya, ya fada a cikin wata makalar da ya rubuta da cewa, shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kasar Sin ta gabatar na neman karfafa mu’ammalar abokan hulda a fannin manufofi, da hade kayayyakin more rayuwa, da ingiza ciniki, da dunkulewar tsarin kudi, gami da tabbatar da fahimtar juna tsakanin mabambantan al’ummu. Wanda a cewarsa, ya sha bamban da ra’ayin kasar Amurka na “Ba ni goyon baya, in ba haka ba, ka zama abokin gaba. ”

  • Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu
  • Shirye-shiryen CGTN Sun Samu Lambobin Yabo A Bikin Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Larabawa

To, idan mun tantance dalilin da ya sa kasar Sin ke samun bambancin ra’ayi, za mu fahimci cewa, hakan na kasantuwa ne bisa ra’ayin kasar na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya”. Wato a ganin kasar Sin, tsakanin mabambantan kasashe akwai matsayi na daidaituwa. Kana duk wadannan kasashe suna da makomar bai daya. Saboda haka, ya kamata su zama tare cikin zaman lafiya, da more hakki na bai daya, da kokarin hadin gwiwa wajen tinkarar kalubaloli, don tabbatar da cikakkiyar walwalar dukkansu. Sa’an nan idan an yi karin nazari kan ra’ayin na kasar Sin, za a gano asalinsa shi ne daga ka’idoji guda 5 na tabbatar da zama tare cikin lumana, da kasar Sin ta gabatar wasu shekaru 70 da suka wuce, wato girmama wa juna ikon mulkin kai da cikakken yankin kasa, da magance kai hari ga juna, da rashin tsoma baki cikin harkokin gida na juna, da kokarin amfanawa juna cikin daidaito, gami da zama tare cikin lumana. Inda ka’idojin 5 sun nuna yadda kasashe masu tasowa suka yi kokarin kare moriyar kai daga wasu kasashen da ke neman yin babakere a duniya, gami da al’adun gargajiya na kasar Sin na kula da sauran mutane kamar yadda aka kula da kai, da kokarin nuna kauna ga makwabta.

A bisa ra’ayi na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”, ya kamata a yi kokarin tabbatar da daidaituwa da cin moriya tare, a tsakanin kasashe daban daban, yayin da suke hadin gwiwa da juna. To, dangane da haka, an samu dimbin shaidu cikin hadin gwiwar Sin da Afirka: Zuwa yanzu, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin ginawa kasashen Afirka layin dogo na tsawon kilomita 6000, da hanyoyin motoci na kilomita 6000, da tashoshin jiragen ruwa da yawansu ya kai kusan 20, da manyan tashoshin samar da wutar lantarki fiye da 80. Haka zalika, kasar ta zuba jari da gina yankunan masana’antu 25 a kasashen Afirka, inda aka dauki ma’aikata ‘yan Afirka dubu 42, da taimakawa kokarin kasashen Afirka na raya bangaren masana’antu, da sauya tsarin tattalin arzikinsu. Ban da haka, na taba gamuwa da dimbin dalibai ‘yan Afirka da suka zo kasar Sin karatu, da ‘yan kasuwa masu yin cinikayya tsakanin bangarorin Sin da Afirka, da kwararru masu fasahar aikin gona na kasar Sin da suke kokarin yada fasahohin noma na zamani a kasashen Afirka, da Sinawa masu zuba jari da masu kamfanoni da suka dade suke zama a nahiyar Afirka, da dai sauransu. Wadannan mutane na kokarin neman cika burikansu, ta hanyar halarta cikin cudanya da hadin gwiwar Sin da Afirka, da ingiza cudanya tsakanin mabambantan al’ummu da al’adu, tare da samar da gudunmowa ga yunkurin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

Hakika, a nawa fahimta, abin da minista Tuggar ke nufi shi ne, ra’ayin kasar Sin kan tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na wasu kasashen dake yammacin duniya, wadanda ke neman kare yanayinsu na babakere a duniya. Amma idan an kwatanta da ra’ayoyin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka, da na kasar Sin, to, za a ga suna da ra’ayi daya. Inda suke neman magance son kai, da ja-in-ja, da tsarin kashin dankali, gami da rungumar ra’ayin zama tare cikin lumana, da hadin gwiwa da amfanin juna, da kuma neman samun ci gaba na bai daya. To, wannan ra’ayi nasu ya nuna hanya mai dacewa da ya kamata a bi, don neman tabbatar da ci gaban duniya, da na harkokin daukacin dan Adam. (Bello Wang)

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Afirka da TuraiAlakar Sin da AfirkaCi gaban Afirka
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Nune-Nunen Shirye-Shiryen CMG Masu Inganci A Kazakhstan Da Tajikistan

Next Post

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

3 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

4 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

5 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

5 days ago
Next Post
Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam'iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

September 7, 2025
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

September 7, 2025
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

September 7, 2025
Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.