• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Bambancin Ra’ayi Na Kasar Sin Dangane Da Tsarin Kasa Da Kasa ?

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Mene Ne Bambancin Ra’ayi Na Kasar Sin Dangane Da Tsarin Kasa Da Kasa ?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin ziyarar Yusuf Maitama Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya, a kasar Sin a kwanan baya, wata maganar da ya fada ya burge ni, inda ya ce, “Yadda kasar Sin ke kallon tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na sauran kasashe: Ba ta kallon duniya a matsayin filin dambarwar siyasa, maimakon haka, tana neman karfafa hadewar yankuna da kasashe, ta shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.”

Wannan bambanci game da kasar Sin da minista Tuggar ya ambata ya samu tabbatuwa ta bakin mutanen sauran kasashe. Misali, Roger McKenzie, wani editan jaridar Morning Star ta kasar Birtaniya, ya fada a cikin wata makalar da ya rubuta da cewa, shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kasar Sin ta gabatar na neman karfafa mu’ammalar abokan hulda a fannin manufofi, da hade kayayyakin more rayuwa, da ingiza ciniki, da dunkulewar tsarin kudi, gami da tabbatar da fahimtar juna tsakanin mabambantan al’ummu. Wanda a cewarsa, ya sha bamban da ra’ayin kasar Amurka na “Ba ni goyon baya, in ba haka ba, ka zama abokin gaba. ”

  • Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu
  • Shirye-shiryen CGTN Sun Samu Lambobin Yabo A Bikin Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Larabawa

To, idan mun tantance dalilin da ya sa kasar Sin ke samun bambancin ra’ayi, za mu fahimci cewa, hakan na kasantuwa ne bisa ra’ayin kasar na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya”. Wato a ganin kasar Sin, tsakanin mabambantan kasashe akwai matsayi na daidaituwa. Kana duk wadannan kasashe suna da makomar bai daya. Saboda haka, ya kamata su zama tare cikin zaman lafiya, da more hakki na bai daya, da kokarin hadin gwiwa wajen tinkarar kalubaloli, don tabbatar da cikakkiyar walwalar dukkansu. Sa’an nan idan an yi karin nazari kan ra’ayin na kasar Sin, za a gano asalinsa shi ne daga ka’idoji guda 5 na tabbatar da zama tare cikin lumana, da kasar Sin ta gabatar wasu shekaru 70 da suka wuce, wato girmama wa juna ikon mulkin kai da cikakken yankin kasa, da magance kai hari ga juna, da rashin tsoma baki cikin harkokin gida na juna, da kokarin amfanawa juna cikin daidaito, gami da zama tare cikin lumana. Inda ka’idojin 5 sun nuna yadda kasashe masu tasowa suka yi kokarin kare moriyar kai daga wasu kasashen da ke neman yin babakere a duniya, gami da al’adun gargajiya na kasar Sin na kula da sauran mutane kamar yadda aka kula da kai, da kokarin nuna kauna ga makwabta.

A bisa ra’ayi na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”, ya kamata a yi kokarin tabbatar da daidaituwa da cin moriya tare, a tsakanin kasashe daban daban, yayin da suke hadin gwiwa da juna. To, dangane da haka, an samu dimbin shaidu cikin hadin gwiwar Sin da Afirka: Zuwa yanzu, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin ginawa kasashen Afirka layin dogo na tsawon kilomita 6000, da hanyoyin motoci na kilomita 6000, da tashoshin jiragen ruwa da yawansu ya kai kusan 20, da manyan tashoshin samar da wutar lantarki fiye da 80. Haka zalika, kasar ta zuba jari da gina yankunan masana’antu 25 a kasashen Afirka, inda aka dauki ma’aikata ‘yan Afirka dubu 42, da taimakawa kokarin kasashen Afirka na raya bangaren masana’antu, da sauya tsarin tattalin arzikinsu. Ban da haka, na taba gamuwa da dimbin dalibai ‘yan Afirka da suka zo kasar Sin karatu, da ‘yan kasuwa masu yin cinikayya tsakanin bangarorin Sin da Afirka, da kwararru masu fasahar aikin gona na kasar Sin da suke kokarin yada fasahohin noma na zamani a kasashen Afirka, da Sinawa masu zuba jari da masu kamfanoni da suka dade suke zama a nahiyar Afirka, da dai sauransu. Wadannan mutane na kokarin neman cika burikansu, ta hanyar halarta cikin cudanya da hadin gwiwar Sin da Afirka, da ingiza cudanya tsakanin mabambantan al’ummu da al’adu, tare da samar da gudunmowa ga yunkurin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

Hakika, a nawa fahimta, abin da minista Tuggar ke nufi shi ne, ra’ayin kasar Sin kan tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na wasu kasashen dake yammacin duniya, wadanda ke neman kare yanayinsu na babakere a duniya. Amma idan an kwatanta da ra’ayoyin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka, da na kasar Sin, to, za a ga suna da ra’ayi daya. Inda suke neman magance son kai, da ja-in-ja, da tsarin kashin dankali, gami da rungumar ra’ayin zama tare cikin lumana, da hadin gwiwa da amfanin juna, da kuma neman samun ci gaba na bai daya. To, wannan ra’ayi nasu ya nuna hanya mai dacewa da ya kamata a bi, don neman tabbatar da ci gaban duniya, da na harkokin daukacin dan Adam. (Bello Wang)

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Afirka da TuraiAlakar Sin da AfirkaCi gaban Afirka
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Nune-Nunen Shirye-Shiryen CMG Masu Inganci A Kazakhstan Da Tajikistan

Next Post

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

2 days ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

3 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

1 week ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Next Post
Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam'iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.