ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Bambancin Ra’ayi Na Kasar Sin Dangane Da Tsarin Kasa Da Kasa ?

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Yayin ziyarar Yusuf Maitama Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya, a kasar Sin a kwanan baya, wata maganar da ya fada ya burge ni, inda ya ce, “Yadda kasar Sin ke kallon tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na sauran kasashe: Ba ta kallon duniya a matsayin filin dambarwar siyasa, maimakon haka, tana neman karfafa hadewar yankuna da kasashe, ta shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.”

Wannan bambanci game da kasar Sin da minista Tuggar ya ambata ya samu tabbatuwa ta bakin mutanen sauran kasashe. Misali, Roger McKenzie, wani editan jaridar Morning Star ta kasar Birtaniya, ya fada a cikin wata makalar da ya rubuta da cewa, shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kasar Sin ta gabatar na neman karfafa mu’ammalar abokan hulda a fannin manufofi, da hade kayayyakin more rayuwa, da ingiza ciniki, da dunkulewar tsarin kudi, gami da tabbatar da fahimtar juna tsakanin mabambantan al’ummu. Wanda a cewarsa, ya sha bamban da ra’ayin kasar Amurka na “Ba ni goyon baya, in ba haka ba, ka zama abokin gaba. ”

  • Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu
  • Shirye-shiryen CGTN Sun Samu Lambobin Yabo A Bikin Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Larabawa

To, idan mun tantance dalilin da ya sa kasar Sin ke samun bambancin ra’ayi, za mu fahimci cewa, hakan na kasantuwa ne bisa ra’ayin kasar na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya”. Wato a ganin kasar Sin, tsakanin mabambantan kasashe akwai matsayi na daidaituwa. Kana duk wadannan kasashe suna da makomar bai daya. Saboda haka, ya kamata su zama tare cikin zaman lafiya, da more hakki na bai daya, da kokarin hadin gwiwa wajen tinkarar kalubaloli, don tabbatar da cikakkiyar walwalar dukkansu. Sa’an nan idan an yi karin nazari kan ra’ayin na kasar Sin, za a gano asalinsa shi ne daga ka’idoji guda 5 na tabbatar da zama tare cikin lumana, da kasar Sin ta gabatar wasu shekaru 70 da suka wuce, wato girmama wa juna ikon mulkin kai da cikakken yankin kasa, da magance kai hari ga juna, da rashin tsoma baki cikin harkokin gida na juna, da kokarin amfanawa juna cikin daidaito, gami da zama tare cikin lumana. Inda ka’idojin 5 sun nuna yadda kasashe masu tasowa suka yi kokarin kare moriyar kai daga wasu kasashen da ke neman yin babakere a duniya, gami da al’adun gargajiya na kasar Sin na kula da sauran mutane kamar yadda aka kula da kai, da kokarin nuna kauna ga makwabta.

ADVERTISEMENT

A bisa ra’ayi na “gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”, ya kamata a yi kokarin tabbatar da daidaituwa da cin moriya tare, a tsakanin kasashe daban daban, yayin da suke hadin gwiwa da juna. To, dangane da haka, an samu dimbin shaidu cikin hadin gwiwar Sin da Afirka: Zuwa yanzu, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin ginawa kasashen Afirka layin dogo na tsawon kilomita 6000, da hanyoyin motoci na kilomita 6000, da tashoshin jiragen ruwa da yawansu ya kai kusan 20, da manyan tashoshin samar da wutar lantarki fiye da 80. Haka zalika, kasar ta zuba jari da gina yankunan masana’antu 25 a kasashen Afirka, inda aka dauki ma’aikata ‘yan Afirka dubu 42, da taimakawa kokarin kasashen Afirka na raya bangaren masana’antu, da sauya tsarin tattalin arzikinsu. Ban da haka, na taba gamuwa da dimbin dalibai ‘yan Afirka da suka zo kasar Sin karatu, da ‘yan kasuwa masu yin cinikayya tsakanin bangarorin Sin da Afirka, da kwararru masu fasahar aikin gona na kasar Sin da suke kokarin yada fasahohin noma na zamani a kasashen Afirka, da Sinawa masu zuba jari da masu kamfanoni da suka dade suke zama a nahiyar Afirka, da dai sauransu. Wadannan mutane na kokarin neman cika burikansu, ta hanyar halarta cikin cudanya da hadin gwiwar Sin da Afirka, da ingiza cudanya tsakanin mabambantan al’ummu da al’adu, tare da samar da gudunmowa ga yunkurin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

Hakika, a nawa fahimta, abin da minista Tuggar ke nufi shi ne, ra’ayin kasar Sin kan tsarin kasa da kasa ya sha bamban da na wasu kasashen dake yammacin duniya, wadanda ke neman kare yanayinsu na babakere a duniya. Amma idan an kwatanta da ra’ayoyin kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka, da na kasar Sin, to, za a ga suna da ra’ayi daya. Inda suke neman magance son kai, da ja-in-ja, da tsarin kashin dankali, gami da rungumar ra’ayin zama tare cikin lumana, da hadin gwiwa da amfanin juna, da kuma neman samun ci gaba na bai daya. To, wannan ra’ayi nasu ya nuna hanya mai dacewa da ya kamata a bi, don neman tabbatar da ci gaban duniya, da na harkokin daukacin dan Adam. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam'iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.