• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere

Ya Ziyarci Jami'an NIS Da Aka Farmake Su A Jigawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa sun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin Nijeriya da ya kai tsawon kilomita sama da 5000 a sassan ƙasar domin zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Jihar Jigawa a yau Asabar domin ta’aziyya da kuma jaje ga jami’an hukumar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a ranar 9 ga Agustan 2022.

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) tare da tawagarsa a fadar mai martaba Sarkin Dutse da ke Jihar Jigawa

A wani jawabi da ya yi wa manema labarai, CGI Isah Jere ya bayyana cewa, “Bari na sake jaddada cewa mun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin ƙasar nan babu fashi, za mu ƙara himma da ƙwazo a wannan bangaren. Za mu cigaba da tabbatar da kare dukkanin iyakokin Nijeriya domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali kasar nan.”

  • Yadda Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Suka Habaka Noma A Nijeriya

Kwanturola Janar na hukumar ta NIS ya sanar da cewa yanzu haka suna amfani da na’urorin zamani wajen inganta aikin tsaron iyakokin kasa.

Isah Jere Idris ya nemi hadin kan jama’a wajen cimma nasarori kan harkokin tsaro, “Muna neman haɗin guiwar jama’a da ‘yan jarida wajen cimma nasarorin inganta tsaro.”

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) da sauran jami’an NIS na reshen Jihar Jigawa

Ya ƙara da cewa yanzu haka hukumar ta maida hankali wajen amfani da fasahar zamani wajen kyautatawa da inganta tsaro a iyakokin kasar nan.

Jere ya ce ya ziyarci Jihar Jigawa ce domin ganawa da jami’ansa na jihar tare da jajanta wa iyalan jami’insa Abdullahi Mohammed da ya rasu a lokacin da yake bakin aikinsa na kare ƙasa.

“Na zo nan Jigawa domin jinjina irin ƙwazo da ƙoƙari da haziƙancin jami’inmu bisa sadaukar da kai da jarumtarsa wajen kare kasar nan da kiyaye kimarta. Za mu ci gaba da tuna Abdullahi Mohammed a matsayin jarumi kuma haziki. Ina tabbatar wa iyalan mamacin cewa tabbas jininsa bai tafi a banza ba. Muna addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa.”

A cewarsa: “Marigayi Abdullahi Mohammed da abokan aikinsa suna sintiri ne a hanyar Galadi zuwa Birniwa a ranar 9 ga watan Agustan 2022 yayin da wasu marasa kishin ƙasa suka kai musu farmaki a yayin da suke bakin aikinsu. Shi Abdullahi da abokan aikinsa irin su Abba Musa Kiyawa (DSI) da Zubairu Garba (AII) sun jajirce tare da mayar da martani ga waɗanda suka kawo musu harin, abin takaici ya gamu da raunuka sakamakon hakan ya rigamu gidan gaskiya.”

Kazalika, Jere ya kai irin wannan ziyarar ta jajantawa ga sauran abokan aikinsu biyu da suka gamu da raunuka a sakamakon harin, “Suna amsar kulawar Likitoci a nan Jigawa. Tun lokacin da na karɓi ragamar shugabanci na mayar sha’anin kula da jin daɗi da walwalar jami’aina a matsayin abu mai matukar muhimmanci a tsare-tsarena.”

Shugaban hukumar ta NIS ula ya kuma shaida cewar, kyautata jin dadi da walwalar jami’an hukumar shi ne ya sanya a gaba kuma ya bai wa muhimmanci domin tabbatar da jami’an na samun yanayin gudanar da aiki yadda ya kamata.

Ya ce, yana tabbatar da kula da jin dadin nasu ne domin ba su ƙwarin guiwar gudanar da ayyukansu yadda ya dace don tabbatar da kare kasa a kowani lokaci, “Kuma na himmatu a wannan fannin zan kuma ci gaba tabbatar da jami’aina na samun kyakkyawar yanayin aiki a kowani lokaci.”

Shugaban ya ƙara da cewa irin wannan kulawar tasa ce ma ta sanya shi da kansa ya kai ziyarar ta’aziyyar jami’insa da ya rasa ransa a fagen aiki tare da ziyarartar wadanda suka jikkata a gadon asibiti duk da tarin ayyukan da suke gabansa amma ya jingine su don kai wannan ziyarar.

Tsaro
CGI Isah Jere Idris yayin da aka tarbe shi a Dutse, Jihar Jigawa

A wani labarin kuma wani kamfanin da ke harkar ƙawance da hukumar ta NIS wato Contect Global Services Ltd ya ba da tallafin naira miliyan huɗu (N4,000,000) ga iyalan mamacin da kuma wadanda suke jinya.

CGI Isah Jere dai ya sake nanata aniyar NIS ta ba da muhimmanci sosai ga tsaron iyakoki domin tallafa wa tsaron ƙasa da samun ci gaba mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Sojoji 2 Kan Zargin Suna Da Hannu A Kisan Wani Malamin Addinin Musulunci A Yobe

Next Post

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

53 minutes ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

3 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

4 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

5 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

17 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

18 hours ago
Next Post
Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.