ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

by Bello Hamza
1 year ago
Shugaban

Biyo bayan kokarin da ake yi na sake farfado da babban wajen da Jiragen Ruwa ke tsayawa wato OMT da ke a Tashar Jiragen Ruwa ta Onne, Babban Jami’i da ke lura da OMT Jim Stewart, ya jinjinawa Shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Qasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho.

Stewart, ya yabawa Dantsoho ne, kan goyon bayan da yake ci gaba da bayar wa da kuma kara inganta ayyukan Hukumar, inda ya ce, NPA a karkashin shugabancin Dantsoho, ya samar da dibin ci gaba ga ci gaban, musamman  babban wajen da Jiragen Ruwa ke tsayawa na Tashoshin Jiragen Ruwan Qasar.

  • Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
  • Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

A cewarsa, Shugaban ya samar da wannan nasarar ce a Tashar Jiragen Ruwa ta Onne, a ranar 16 na watan Afirilun 2025 wanda hakan ya nuna karin samun ci gaba da na wajen wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci, a Afirka ta Yamma.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, isowar Jirgin Ruwa na daya daga cikin manyan Kafanonin Jiragen Ruwa da ke yin jigilar kaya da ke a yankin Asia ga babban wajen da Jiragen Ruwa ke tsayawa a OMT, hakan ya kara nuna sake farfadowar babban wajen tsayawar Jiragen.

Jirgin Ruwan Kamfanin ya iso Tashar ta Onne ne, dauke da Kwantainoni1, 250, inda kuma ya aka loda masa wasu Kwantainoni 1,619

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A jawabinsa a wajen tarbar Jirgin Ruwan na na yankin Asia Jim Stewart, ya bayyana jin dadinsa ga Hukumar ta NPA, bisa goyon bayan da ta bayar wajen samar da kyakyawan yanayi a babban wajen da Jiragen Runwan na Tashar Onne suke tsayawa.

“Muna da kyakaywar dangantakar gudanar da ayyuka da Manajan Tashar ta Onne Mista Abdulrahmon Hussain da kuma sauran ‘yan tawagar Hukumar ta NPA, “Inji Stewart.

Ya ci gaba da cewa, a karkashin shugabancin shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho, wanda kuma kashin bayan duk wata nasara da muka zamu.

“Sake farfado da babban wajen tsayawar Jiragen Ruwan a Tashar Onne, hakan ya kara mana kwarin Guiwa”. A cewar Stewart.

Kazalika, Stewart ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kara samar da wadatattun kudade domin a kara fadada aikin yasar Gulnin da ke a Tashar ta Onne.

Tashar ta Onne, musamman domin a samu karin yawan Jiragen Ruwa masu tsayawa a Tashar, wanda hakan zai kuma kara taimaka wa, wajen bunkasa hada-hadar kasuwanci a Tashar.

“Mun shirya tsaf, domin tarbar Jiragen Ruwa masu yawa da suka, amma domin mu ci gaba da cin gajiyar da ta kamata a Tashar ta Onne, akwai matukar bukatar a mayar da hankali wajen kara fadada yin haka a Gulbin da ke a Tashar, ” Inji Stewart.

“Mun kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kara taimaka wa Hukumar ta NPA da kudaden da suka kamata, musamman domin a kara fadada hakar Gubin na Tashar Onne,” A cewar Stewart.

 

Ya bayyana cewa, biyo bayan isowar da Jirgin Ruwa na Kota Cempaka ya yi a Tashar ta Onne, a shekarar da ta gabata, wannan nasarar ta nuna irin yadda ake ci gaba da samar da dabarun zuba hannun jari a Tashar ta Onne da kuma yadda aka kara mayar da hankali, wajen kara inganta ayyukan na Tashar.

Kazalika, Stewart ya jaddda mahimmancin zamanantar da Tashar ta Onne, ta hanyar gyare-gyaren da ake yi a Tashar, matsayin wata manufa ta rage cunkoson Jiragen Ruwa da ke tsayawa Tashar.

 

Ya yi nuni da cewa, ganin yadda irin wadannan manyan Jiragen Ruwa suka fara isowa Tashar ta Onne, hakan kara taimaka wa, wajen kara bunka tattalin arziki ga Tashoshin Jiragen Ruwan kasar nan,

Ya kara da cewa, hakan zai kuma kara taimaka wa, wajen ragewa ‘yan kasuwar da ke shigoa da kayan zuwa cikin kasar nan da kuma rage cazarsu kudin harajin fitar da kaya zuwa ketare.

 

“Wannan nasarar bai wai kawai ta shafi Tashar ta Onne bane kadai, har da daukacin tattalin arzikin kasar nan, kuma sake farfadowar Tashar ta Onne, za ta kara bayar da wata damar kara shigowar Jiragen Ruwa cikin kasar nan, wanda hakan zai kuma kara samarwa da Nijeriya, da wasu kudaden shiga, “Inji Stewart,

Shi kuwa a na sa jawabin Hukumar ta NPA wani babban Direban Jirgin Ruwa a Tashar ta Onne Yakubu Ezra, ya jaddada cewa, Hukumar ta NPA, a shiraye take wajen karbar duk wasu Jiragen Ruwa da za su sauka a Tashar ta Onne.

“An tanadar da isassun kayan aiki na fasahar zamani Tashoshin Jiragen Ruwan kasar nan, musamman domin a Jiragen Ruwan su rinkaa tsakyawa a cikin sauki, tare da kuma bai wa ma’aikatan horon da ya dace, “ Inji Yakubu.

A cewasa, samun nasarar ta isowar Jirgin Ruwan na Kota Carum alamu ne da nuna irin karfin Tashar ta Onne da kuma irin kwarewar da Tashar take da shi.

Ganin yadda Jiragen Ruwa da dama daga Afrika ta Yamma ke shirin isowa Tashar ta Onne, hakan ya kara nuna irin ingantattun kayan aiki da damarun da aka samar a Tashar, wanda hakan zai kara bayar da dama wajen kara janyo zuwan Jirage da kasa da kasa, zuwa Tashar.

Shugaban
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.