• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa babu inda gwamnatin sa ta hana yi ko sayar da biredi a duk faɗin jihar.

Wannan ya biyo bayan wata sanarwa ce da ƙungiyar masu gidajen biredi ta jihar Zamfara ta fitar, inda suka shelanta dakatar da gasa biredin sakamakon haramta tallar sa da gwamnatin ta yi a bisa babura, wanda kuma gwamnatin ta ce ta yi haka ne don ta katse hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda biredin.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Haɗin Gwiwa Da Ƙasar Sweden Kan Haƙar Ma’adanai Da Noma

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa gwamnatin ba ta ɗauki wannan matakin da wata mummunar manufa b ne, illa don ta toshe hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda kayan masarufi a duk faɗin jihar.

Sanarwar ta Idris ta ƙara da cewa gwamnatin ta haramta sayar da biredi da man fetur a wuraren da ta’addancin ya yi ƙamari ne don a toshe hanyoyin da ‘yan ta’addan ke samun kayan masarufi.

Sanarwar ta ƙara sa cewa, “Gwamnatin jijar Zamfara na so ta yi ƙarin haske game da surutan sa ke yawo, inda ake zargin cewa gwamnatin ta hana masu gidaje biredi yi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

“Gwamnatin na ƙalubalantar waɗannan labarai da cewa ba gaskiya ba ne, wanda ke kuma jawo ruɗani a tsakanin jama’a da su kan su masu gidajen biredin.

“Gwamnatin jihar Zamfara ba ta da wata niyya ta tsoma baki a harkar gasawa ko sayar da biredi, wanda biredi a yanzu ya zama shi ne kusan abincin kowane gida.

“Bugu da ƙari, mu na so mu tabbatar wa al’umma cewa kullum ƙoƙarin gwamnati, shi ne fito da hanyoyin da za ta inganta harkokin kasuwanci da hanyoyin cin abinci ga al’ummar ta. Mu na sane da irin gudumawar da ƙananan masana’antu ke bayarwa ga ci gaban tattalin arziki, kuma mun jajirce wajen ganin mun ƙarfafa masu gwiwa don cimma nasarar su.

“Kuma duk da haka, mun fito da wasu hanyoyi da dama na yaƙar ‘yan ta’adda masu kawo mana ruɗani a wasu sassan jihar nan.

“Waɗannan hanyoyi kuwa, sun haɗa da haramta sayar da biredi da man fetur a wasu wurare da ba a natsu da su ba, ba domin komai ba, sai don a takura wa waɗannan shaiɗanu, domin sun dogara ne da waɗannan muhimman abubuwa wajen aiwatar da Ta’addancin su.

“Gwamnatin jihar Zamfara na da fatan cewa sakamakon aiwatar da wannan haramci, za ta iya dawo da zaman lafiya a waɗannan wurare, don kare rayuka da dukiyar jama’a. Wannan haramci da aka ambata, yana daga dabarun da ake sa ran cimma nasarar wannan yaƙi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BurodiDaudaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD

Next Post

Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

Related

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

2 minutes ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

2 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

3 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

11 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

12 hours ago
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

14 hours ago
Next Post
Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

LABARAI MASU NASABA

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.