• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

by Leadership Hausa
2 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa babu inda gwamnatin sa ta hana yi ko sayar da biredi a duk faɗin jihar.

Wannan ya biyo bayan wata sanarwa ce da ƙungiyar masu gidajen biredi ta jihar Zamfara ta fitar, inda suka shelanta dakatar da gasa biredin sakamakon haramta tallar sa da gwamnatin ta yi a bisa babura, wanda kuma gwamnatin ta ce ta yi haka ne don ta katse hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda biredin.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Haɗin Gwiwa Da Ƙasar Sweden Kan Haƙar Ma’adanai Da Noma

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa gwamnatin ba ta ɗauki wannan matakin da wata mummunar manufa b ne, illa don ta toshe hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda kayan masarufi a duk faɗin jihar.

Sanarwar ta Idris ta ƙara da cewa gwamnatin ta haramta sayar da biredi da man fetur a wuraren da ta’addancin ya yi ƙamari ne don a toshe hanyoyin da ‘yan ta’addan ke samun kayan masarufi.

Sanarwar ta ƙara sa cewa, “Gwamnatin jijar Zamfara na so ta yi ƙarin haske game da surutan sa ke yawo, inda ake zargin cewa gwamnatin ta hana masu gidaje biredi yi a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

“Gwamnatin na ƙalubalantar waɗannan labarai da cewa ba gaskiya ba ne, wanda ke kuma jawo ruɗani a tsakanin jama’a da su kan su masu gidajen biredin.

“Gwamnatin jihar Zamfara ba ta da wata niyya ta tsoma baki a harkar gasawa ko sayar da biredi, wanda biredi a yanzu ya zama shi ne kusan abincin kowane gida.

“Bugu da ƙari, mu na so mu tabbatar wa al’umma cewa kullum ƙoƙarin gwamnati, shi ne fito da hanyoyin da za ta inganta harkokin kasuwanci da hanyoyin cin abinci ga al’ummar ta. Mu na sane da irin gudumawar da ƙananan masana’antu ke bayarwa ga ci gaban tattalin arziki, kuma mun jajirce wajen ganin mun ƙarfafa masu gwiwa don cimma nasarar su.

“Kuma duk da haka, mun fito da wasu hanyoyi da dama na yaƙar ‘yan ta’adda masu kawo mana ruɗani a wasu sassan jihar nan.

“Waɗannan hanyoyi kuwa, sun haɗa da haramta sayar da biredi da man fetur a wasu wurare da ba a natsu da su ba, ba domin komai ba, sai don a takura wa waɗannan shaiɗanu, domin sun dogara ne da waɗannan muhimman abubuwa wajen aiwatar da Ta’addancin su.

“Gwamnatin jihar Zamfara na da fatan cewa sakamakon aiwatar da wannan haramci, za ta iya dawo da zaman lafiya a waɗannan wurare, don kare rayuka da dukiyar jama’a. Wannan haramci da aka ambata, yana daga dabarun da ake sa ran cimma nasarar wannan yaƙi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar
Manyan Labarai

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Next Post
Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Dauda

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.