• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari

by Sadiq
2 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gode wa ministocinsa da ma’aikatan fadar shugaban kasa da suka yi aiki tare da shi cikin shekaru takwas da suka gabata.

Shugaban kasar wanda zai mika wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu mulki a ranar 29 ga watan Mayu, ya ce yana alfahari da cewa shi da mukarrabansa sun bai ‘yan Nijeriya iya gudunmawarsu.

  • Tabbas Za’a Karyata Jita-Jitar Dake Shafawa Jihar Tibet Bakin Fenti
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 96 Da Ake Zargi Da Aikata Laifuka A Kano

A taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) da aka gudanar a zauren majalisar dokoki, shugaban ya mika godiyarsa ga dukkanin ministocin bisa jajircewar da suka yi wajen cimma manufofin gwamnatin, inda ya bukaci a marawa shugaban kasa mai jiran gado baya.

“Ina alfahari da cewa mun yi iya Kokarinmu,” an ruwaito shugaban kasar yana fadar haka a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya fitar.

Shugaban ya umarci ministocin da su gyara ayyukansu tare da kaucewa gaggawar da ka iya kawo cikas ga ayyukan alheri da suka yi tsawon shekaru.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

“Sakamakon shekarun da muka yi tare, tsawon shekaru bakwai da rabi, mun bambanta kan batutuwa da yawa. Ina rokon mu fahimci cewa wadannan mukamai sun kasance na gama gari ne, kuma babu wanda ya isa ya ci gaba da koke-koke, ko ci gaba da wadannan bambance-bambance.

“Ga wadanda ba za su kasance cikin gwamnati kai tsaye ba, na san ina daya daga cikin irin wadannan, ina rokon mu ci gaba da bayar da goyon bayanmu, ta kowace hanya, idan babbar jam’iyyarmu ta kira mu, wacce ta ba mu damar tsayawa, kuma dole ne mu ci gaba da mara mata baya ta kowace hanya da za mu iya,” in ji shi.

Shugaban ya danganta duk wani kyakkyawan aiki da fatan alheri da gwamnatin ta samu da taimakon Allah, inda ya kara da cewa, “Ina kuma gode wa Allah da Ya ba mu karfin gwiwa da ya hada mu baki daya.

“Zan kuma yi farin cikin yin abubuwa da dama da ban samu ba tun ranar 29 ga watan Mayu, 2015, daya daga cikin irin wannan shi ne lokacin da na fi so na kula da shanuna.

“Ina yi mana fatan alheri kuma ina fatan mu ji labari mai dadi a duk lokacin da aka ambaci sunayenmu. Na gode kuma Allah ya albarkaci Tarayyar Nijeriya,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.