• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mun Yi Iya Kokarinmu Wajen Shugabancin Nijeriya —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gode wa ministocinsa da ma’aikatan fadar shugaban kasa da suka yi aiki tare da shi cikin shekaru takwas da suka gabata.

Shugaban kasar wanda zai mika wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu mulki a ranar 29 ga watan Mayu, ya ce yana alfahari da cewa shi da mukarrabansa sun bai ‘yan Nijeriya iya gudunmawarsu.

  • Tabbas Za’a Karyata Jita-Jitar Dake Shafawa Jihar Tibet Bakin Fenti
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 96 Da Ake Zargi Da Aikata Laifuka A Kano

A taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) da aka gudanar a zauren majalisar dokoki, shugaban ya mika godiyarsa ga dukkanin ministocin bisa jajircewar da suka yi wajen cimma manufofin gwamnatin, inda ya bukaci a marawa shugaban kasa mai jiran gado baya.

“Ina alfahari da cewa mun yi iya Kokarinmu,” an ruwaito shugaban kasar yana fadar haka a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina ya fitar.

Shugaban ya umarci ministocin da su gyara ayyukansu tare da kaucewa gaggawar da ka iya kawo cikas ga ayyukan alheri da suka yi tsawon shekaru.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

“Sakamakon shekarun da muka yi tare, tsawon shekaru bakwai da rabi, mun bambanta kan batutuwa da yawa. Ina rokon mu fahimci cewa wadannan mukamai sun kasance na gama gari ne, kuma babu wanda ya isa ya ci gaba da koke-koke, ko ci gaba da wadannan bambance-bambance.

“Ga wadanda ba za su kasance cikin gwamnati kai tsaye ba, na san ina daya daga cikin irin wadannan, ina rokon mu ci gaba da bayar da goyon bayanmu, ta kowace hanya, idan babbar jam’iyyarmu ta kira mu, wacce ta ba mu damar tsayawa, kuma dole ne mu ci gaba da mara mata baya ta kowace hanya da za mu iya,” in ji shi.

Shugaban ya danganta duk wani kyakkyawan aiki da fatan alheri da gwamnatin ta samu da taimakon Allah, inda ya kara da cewa, “Ina kuma gode wa Allah da Ya ba mu karfin gwiwa da ya hada mu baki daya.

“Zan kuma yi farin cikin yin abubuwa da dama da ban samu ba tun ranar 29 ga watan Mayu, 2015, daya daga cikin irin wannan shi ne lokacin da na fi so na kula da shanuna.

“Ina yi mana fatan alheri kuma ina fatan mu ji labari mai dadi a duk lokacin da aka ambaci sunayenmu. Na gode kuma Allah ya albarkaci Tarayyar Nijeriya,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariMika MulkiMinistociMulkiShugabanciTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Bukatar Wani Tsarin Cinikin Kasa Da Kasa Mai Adalci Dake Iya Yaki Da Babakeren Dalar Amurka.

Next Post

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Related

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

1 hour ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

2 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

6 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

21 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

22 hours ago
Next Post
Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.