• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoto da Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno, BOSEMA, ta fitar ta ce adadin wadanda suka mutu a sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a garin Gwoza da ke Karamar Hukumar Gwoza a ranar Asabar zuwa yanzu ya kai mutum 18, inda aka tabbatar da mutum 19 kuma sun samu raunuka.

LEADERSHIP HAUSA ta ce jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, ASP Nahum Daso, a ranar Asabar ya tabbatar da mutuwar mutane 8 tare da wasu mutane 15 da suka samu raunuka a yayin harin kunar bakin waken.

  • Mutun 6 Sun Mutu Harin Ƙunar Ɓakin Wake a Borno
  • Boko Haram Sun Sace Wani Alkali Da Matarsa Tare Da Awon-Gaba Da Wasu Mutane A Borno

Kazalika, wani karin bayani da Darakta Janar na BOSEMA, Dr. Barkindo Saidu, ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a ranar Lahadin ya bayyana cewa adadin wadanda suka mutu a daren ranar Asabar ya kai 18, yayin da 19 da suka samu raunuka daban-daban inda yanzu haka suna jinya a asibitocin Maiduguri.

Dr. Saidu, ya ce akan idonsa, da misalin karfe 3 na yammacin ranar Asabar, bam na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata ‘yar kunar bakin wake ta tayar da bam a wajen bikin aure.

Ya kara da cewa sama da mutane 30 ne abin ya shafa tare da raunuka daban-daban inda wasu kuma suka mutu nan take.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

Dr. Saidu ya ce bayan ‘yan wasu mintoci, an sake samun fashewar wani abun fashewa a kusa da babban asibitin da ke garin.

A safiyar Lahadi, wata majiya daga BOSEMA da ta nemi bukaci a sakaya sunanta ta ce, adadin yawan mutanen suka mutu na iya zarce 18 idan aka yi la’akari da girman raunukan da suka samu.

A gefe guda kuma wata majiyar ta yi zargin cewa sama da gawar mutane 25 aka dauko daga wurare uku kafin sojoji su rufe hedikwatar karamar hukumar tare da sanya dokar hana fita da yammacin ranar Asabar.

Wakilinmu LEADERSHIP HAUSA ya ruwaito cewa, Gwoza na daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kwace a baya inda suka ayyana ta a matsayin mallakin su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoGwozaHariKunar bakin wake
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin MDD Ya Bukaci Daukar Matakan Gaggawa Na Dawo Da Nijeriya Turbar Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa (SDG)

Next Post

“Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne”

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

18 hours ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

20 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

20 hours ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

21 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

1 day ago
Next Post
“Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne”

"Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne"

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.