• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

by Sadiq
2 years ago
NAHCON

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta yi amai ta lashe kan alkawarin da ta yi na cewa maniyyata ba za su biya karin kudi ba kan karin dala 250 da aka yi na jigilar jiragen sama.

An bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na cikin gida da ke gudanar da aikin Hajji sun bukaci a kara kudin aikin Hajji da dala 250, sakamakon rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan, wanda zai bukaci karin lokacin zuwa kasar Saudiyya.

  • Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa
  • An Ci Tarar Kamfanin Facebook $1.3 Biliyan

An rufe sararin samaniyar Sudan tun bayan barkewar rikici a watan Afrilu.

Sai dai da yake jawabi a Abuja yayin wani atisayen da aka shirya wa ma’aikatan NAHCON da hukumar alhazai ta jiha da masu gudanar da yawon bude ido masu zaman kansu, Zikrullah Hassan shugaban hukumar NAHCON ya bada tabbacin cewa ba za a bukaci maniyyatan su biya karin kudin ba.

“Kamfanonin jiragenmu na cikin gida bayan tattaunawa da dama sun amince da dala $250 a matsayin karin kudin tikitin jirgi domin gudanar da aikin na bana. Har yanzu muna neman duk hanyoyin da za mu warware wannan tsaiko. Har yanzu muna ba da gudummawa sosai don ganin an gaggauta warware rikicin Sudan ta yadda sararin samaniya zai ya bude kuma a daina kashe-kashen da ake yi wa al’ummar Sudan.”

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

“A NAHCON, muna neman dukkan hanyoyin da za mu tabbatar mun warware matsalar wannan karin kudin. Mun yanke shawarar cewa, ba za a bukaci maniyyata su biya karin kudade a hannun hukumomin alhazai na jiharsu ba. Ba za su bukaci karin kudi ba, ”in ji shi.

Sai dai a wata sanarwa a ranar Litinin, mataimakin daraktan yada labarai na NAHCON, Moisa Ubandawaki, ya ce hukumar ta yanke shawarar cewa maniyyatan za su biya kashi 40 cikin 100 na karin kudin jirgi bayan gwamnatin tarayya ta tallafa wa kamfanonin jiragen sama don yin jigilarsu.

“Hakan zai kara rage tsadar kudin jigilar maniyyatan Nijeriya. A baya dai gwamnati ta yi watsi da kashi 65% na kudin jiragen sama domin rage farashin aikin Hajji. Tare da wannan ci gaban, Karin dala 250 da aka tattauna da kamfanonin jiragen sama za a rage dala 55, ”in ji sanarwar.

“An kiyasta kowane mahajjaci zai biya dala 117, Hukumar ta yanke shawarar rage alawus na alhazai na 2023.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.