ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

by Sadiq
3 years ago
NAHCON

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta yi amai ta lashe kan alkawarin da ta yi na cewa maniyyata ba za su biya karin kudi ba kan karin dala 250 da aka yi na jigilar jiragen sama.

An bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na cikin gida da ke gudanar da aikin Hajji sun bukaci a kara kudin aikin Hajji da dala 250, sakamakon rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan, wanda zai bukaci karin lokacin zuwa kasar Saudiyya.

  • Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa
  • An Ci Tarar Kamfanin Facebook $1.3 Biliyan

An rufe sararin samaniyar Sudan tun bayan barkewar rikici a watan Afrilu.

ADVERTISEMENT

Sai dai da yake jawabi a Abuja yayin wani atisayen da aka shirya wa ma’aikatan NAHCON da hukumar alhazai ta jiha da masu gudanar da yawon bude ido masu zaman kansu, Zikrullah Hassan shugaban hukumar NAHCON ya bada tabbacin cewa ba za a bukaci maniyyatan su biya karin kudin ba.

“Kamfanonin jiragenmu na cikin gida bayan tattaunawa da dama sun amince da dala $250 a matsayin karin kudin tikitin jirgi domin gudanar da aikin na bana. Har yanzu muna neman duk hanyoyin da za mu warware wannan tsaiko. Har yanzu muna ba da gudummawa sosai don ganin an gaggauta warware rikicin Sudan ta yadda sararin samaniya zai ya bude kuma a daina kashe-kashen da ake yi wa al’ummar Sudan.”

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

“A NAHCON, muna neman dukkan hanyoyin da za mu tabbatar mun warware matsalar wannan karin kudin. Mun yanke shawarar cewa, ba za a bukaci maniyyata su biya karin kudade a hannun hukumomin alhazai na jiharsu ba. Ba za su bukaci karin kudi ba, ”in ji shi.

Sai dai a wata sanarwa a ranar Litinin, mataimakin daraktan yada labarai na NAHCON, Moisa Ubandawaki, ya ce hukumar ta yanke shawarar cewa maniyyatan za su biya kashi 40 cikin 100 na karin kudin jirgi bayan gwamnatin tarayya ta tallafa wa kamfanonin jiragen sama don yin jigilarsu.

“Hakan zai kara rage tsadar kudin jigilar maniyyatan Nijeriya. A baya dai gwamnati ta yi watsi da kashi 65% na kudin jiragen sama domin rage farashin aikin Hajji. Tare da wannan ci gaban, Karin dala 250 da aka tattauna da kamfanonin jiragen sama za a rage dala 55, ”in ji sanarwar.

“An kiyasta kowane mahajjaci zai biya dala 117, Hukumar ta yanke shawarar rage alawus na alhazai na 2023.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.