• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan

by Abubakar Abba
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya tare da kamfanin sarrafa takin zamani ‘Fundação Getulio Bargas’ na Kasar Brazil, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sarrafa takin zamani da samar da ingantacen Iri da kuma kudade ga fannin aikin noma a Nijeriya.

Sun sanya hanun ta hanyar ma’aikatar samar da wadataccen abinci na wannan kasa.

  • Halartar Shugaba Xi Taron APEC Da G20, Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil Sun Kasance Wata Hanyar Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa
  • An Yi Wa Shugaban Ƙasar Brazil Lula Da Silva Tiyatar Ƙwaƙwalwa 

Hakan na kunshen ne cikin sanarwar da fadar shugaban kasa ta fitar, wacce Daraktan Yada Labarai da Hurda da Jama’a; Abiodun Oladunjoye ya fitar a Abuja.

Sanarwar ta bayyana cewa, Babban Sakataren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wataceccen Abinci, Farfesa Carlos Iban Simonsen ne ya rabbata hannun a madadin gwamnatin tarayya.

An rattaba hannun ne, a Birnin Rio de Janeiro na kasar ta Brazil a bayan fagen taron shugabanin kasashen duniya 20 masu karfin tattalin arziki a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Kazalika, sanarwar ta sanar da cewa; rattaba hannun ya bode wani sabon fage a tsakanin Nijeriya da aikin da ake yi na amfani da fasahar zamani, don kara bunkasa fannin aikin noma a fadin wannan kasa.

A cewar sanarwar, aikin wanda aka faro tun a shekarar 2018, zai lashe kimanin dala biliyan 1.2, wanda kuma da ma hadaka ce tsakanin Nijeriya da kasar ta Brazil.

Haka zalika, an tsara aikin ne don kara habaka fannin aikin noma na kasar nan, ta hanyar yin amfani da kwararrun da suka fito daga Kasar Brazil.

Har wa yau, sanarwar ta sanar da cewa; bankin Deutsche na inganata aikin noma ta hanyar amfani da fasahar zamani da kuma yada ilimin aikin noman nan da zuwa shekaru goma masu zuwa.

Nan da shekaru biyar masu zuwa, aikin zai gano tare kuma da tallafawa aikin noma a kananan hukumomi 774 tare da bai wa manoman tallafin kudi, domin kara habaka fannin aikin noma da tattalin arziki.

Fashedemi ya sanar da cewa, wannan hadaka; za ta bai wa Kasar Brazil damar jawo Nijeriya a jiki, musamman don gaggauta bunkasa fannin aikin noma a kasar.

A cewar tasa, ta hanyar haka ne za mu samu damar fito da albarkar da ke fannin zuba hannun jari a manyan ayyuka, musamman don samar da wadataccen abinci.

A karkashin yarjejeniyar, masu zaman kansu a fannin sarrafa takin zamani da samar da ingantaccen Iri, ana sa ran za su samu kudaden shiga kimanin dala biliyan 4.3.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Brazil
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Next Post

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

14 hours ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

15 hours ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.