ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan

by Abubakar Abba
11 months ago
Brazil

Gwamnatin tarayya tare da kamfanin sarrafa takin zamani ‘Fundação Getulio Bargas’ na Kasar Brazil, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sarrafa takin zamani da samar da ingantacen Iri da kuma kudade ga fannin aikin noma a Nijeriya.

Sun sanya hanun ta hanyar ma’aikatar samar da wadataccen abinci na wannan kasa.

  • Halartar Shugaba Xi Taron APEC Da G20, Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil Sun Kasance Wata Hanyar Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa
  • An Yi Wa Shugaban Ƙasar Brazil Lula Da Silva Tiyatar Ƙwaƙwalwa 

Hakan na kunshen ne cikin sanarwar da fadar shugaban kasa ta fitar, wacce Daraktan Yada Labarai da Hurda da Jama’a; Abiodun Oladunjoye ya fitar a Abuja.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta bayyana cewa, Babban Sakataren Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wataceccen Abinci, Farfesa Carlos Iban Simonsen ne ya rabbata hannun a madadin gwamnatin tarayya.

An rattaba hannun ne, a Birnin Rio de Janeiro na kasar ta Brazil a bayan fagen taron shugabanin kasashen duniya 20 masu karfin tattalin arziki a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Kazalika, sanarwar ta sanar da cewa; rattaba hannun ya bode wani sabon fage a tsakanin Nijeriya da aikin da ake yi na amfani da fasahar zamani, don kara bunkasa fannin aikin noma a fadin wannan kasa.

A cewar sanarwar, aikin wanda aka faro tun a shekarar 2018, zai lashe kimanin dala biliyan 1.2, wanda kuma da ma hadaka ce tsakanin Nijeriya da kasar ta Brazil.

Haka zalika, an tsara aikin ne don kara habaka fannin aikin noma na kasar nan, ta hanyar yin amfani da kwararrun da suka fito daga Kasar Brazil.

Har wa yau, sanarwar ta sanar da cewa; bankin Deutsche na inganata aikin noma ta hanyar amfani da fasahar zamani da kuma yada ilimin aikin noman nan da zuwa shekaru goma masu zuwa.

Nan da shekaru biyar masu zuwa, aikin zai gano tare kuma da tallafawa aikin noma a kananan hukumomi 774 tare da bai wa manoman tallafin kudi, domin kara habaka fannin aikin noma da tattalin arziki.

Fashedemi ya sanar da cewa, wannan hadaka; za ta bai wa Kasar Brazil damar jawo Nijeriya a jiki, musamman don gaggauta bunkasa fannin aikin noma a kasar.

A cewar tasa, ta hanyar haka ne za mu samu damar fito da albarkar da ke fannin zuba hannun jari a manyan ayyuka, musamman don samar da wadataccen abinci.

A karkashin yarjejeniyar, masu zaman kansu a fannin sarrafa takin zamani da samar da ingantaccen Iri, ana sa ran za su samu kudaden shiga kimanin dala biliyan 4.3.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.