Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RA'AYINMU

Batun Gyaran Titunan Nijeriya

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in RA'AYINMU
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A makon da ya gabata, aka fara tataburza kan wani batu da ya kunna kai na karin farashin man fetur da Majalisar Dattawa ke yunkurin yi; lamarin da ya jefa al’ummar kasar nan, musamman talakawa cikin zulumi da fargabar halin da za su iya tsintar kansu matukar aka cimma nasarar kara farashin litar man daga naira 145 zuwa 150.

Ba batun kara kudin alkalaminmu zai yi magana a kai ba – tun da Majalisar Dattawa ta fito fili karara tare da shelanta cewar an yi mata mummunar fahimta, kuma an murguda labarin yadda ‘yan kasa suka rika kallon sa a bai-bai – illa iyaka irin tsoro da fargabar da suka cika zukatan ‘yan Nijeriya a daidai lokacin da maganar ta kunno kai.

samndaads

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, mai wakiltar Kano ta Kudu, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Kula da Titunan Nijeriya a Majalisar Dattawa, ya gabatar da kudurin yin doka kan Tsarin Farfado da titunan Nijeriya da yanzu haka suke cikin mummunan yanayi, wanda a dalilin haka kullum cikin kashe matafiya suke – talakawa wadanda ba za su iya biyan kudin jirgi ba.

Kabiru Gaya, wanda ya zagaya kusan dukkanin titunan da ke fadin Tarayya kasar nan, ya kuma ganewa idonsa halin da suke ciki, saboda haka ya nemi masu ruwa da tsaki a harkar Sufuri da su bullo da wata hanya wadda za ta bawa Gwamnati damar gyaran wadannan titununa cikin sauki – shi ya sa ya nemi a yi doka a Majalisa ta musamman da za ta rika tattauna halin da manyan hanyoyinmu suke ciki.

A halin da ake ciki, hakika titunan kasar nan suna bukatar kyakkyawar kulawa. Akwai kunya matuka game da yanayin tsarin sufuri a Nijeriya. Manyan titunanmu da suka hada da Arewa Maso Gabas, Arewa Maso Yamma, Arewa Ta Tsakiya duk a lalace suke, titi daya ne tal, Abuja-Kaduna ya ci arzikin gyaran faci-faci sakamakon kwaskwarimar da aka yi wa Filin Jirgi na Abuja, amma daga Kaduna zuwa Kano, duk wanda ya kama hanya ransa idan ya yi dubu sai ya baci. Haka lamarin yake a manyan titunan da suka hada Arewa da Kudu, matafiya kullum cikin zulumin bin hanya suke saboda rashin kyawu. Duk da cewa kasar nan Allah ya yi mata arzikin da za ta iya mayar da titunanta tamkar na Dubai ko Saudiyya ba tare da an rika karbar naira biyar daga farashin litar mai ba.

Gwamnati mai ci a yanzu, watau ta APC, karkashin Shugabancin Muhammadu Buhari ta taka rawar ganin matuka wajen kwato makudan kudaden da wasu tsiraru suke kwashe (a yaki da cin hanci da rashawa), ire-iren wadannan kudade suna nan jibge, babu wanda ya san halin da suke ciki. Wasu ma marayu ne domin har yanzu ba a gama gano hakikanin mamallakansu ba, me zai hana a yi amfani da su wajen ci gaban kasa maimakon ajiye su a lalitar banza?

An dade ana gafara sa, amma ‘yan Nijreriya ba su hango kaho ba. A daidai wannan lokacin, mutane suna shan wahala, talauci da fatara kullum karuwa suke yi, mai ci sau uku a rana ya dawo sau biyu, wani ma da kyar yake samun ci sau daya.

Gyaran tituna abu ne mai kyau, amma za a iya yin sa ba tare da an tsauwalawa talakawa ba, Nijeriya kasa ce ma arziki, da za ta iya yin dukkan abinda ta ga dama matukar tana da bukatar hakan.

Matakin da Sanatoci suka dauka na cewar ba kudin man za a kara ba lallai abin yabawa ne, domin kara kudin man fetur ka iya zama silar karuwar farashin kayayyakin harkokin yau da kullum. Muna sane da cewar tun daga lokacin da aka janye tallafin man fetur, wanda ya janyo farashinsa karuwa da kashi 47%, dukkanin kayan amfanin yau da kullum sai da farashinsu ya ninka, domin man fetur na cikin manyan sinadaren da tashin farashinsu babbar illa ce ga rayuwar talaka.

Idan har da gaske gyaran titunan ake so a yi, akwai hanyoyi da yawa wadanda suka dace ba tare da an tsauwalawa talakawa ba, domin mun ga yadda aka gyara titin Abuja zuwa Kaduna cikin kwana 50 kacal, ba domin talaka ba, sai don kusoshin gwamnati da gyaran filin jirgin Abuja ya hana jiragensu sauka a Birnin Tarayya sai a Kaduna.

SendShareTweetShare
Previous Post

DAUSAYIN MUSULUNCI: Hukunce-Hukuncen Azumin Ramadan A Takaice (2)

Next Post

BULALIYA: Haramtacciyar Jamhuriyar Biyafara: Bukatar Ci Gaba Da Zama Hadaddiyar Kasa

RelatedPosts

Dambarwar Najeriya Cikin Shekaru 60: Murna Ya Kamata Mu Yi Ko Kuka?

Yayin Da Nijeriya Ta Cika Shekaru 60 Da ‘Yancin Kai…

by Muhammad
4 months ago
0

A jiya ne Nijeriya ta yi bikin cika shekaru 60...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Cibiyar Jinkan Tsofaffi – Minista Sadiya

Kafa Hukumar Kula Da Nakassasun Nijeriya Da Dawo Da Martabarsu

by Muhammad
4 months ago
0

A ranar Litinin, 24 ga Agusta na 2020 ne, Shugaban...

Bashin NIRSAL: Anya Talaka Na Da Rabo A Ciki Kuwa?

Bashin NIRSAL: Anya Talaka Na Da Rabo A Ciki Kuwa?

by Muhammad
6 months ago
0

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya a karkashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari ta...

Next Post

BULALIYA: Haramtacciyar Jamhuriyar Biyafara: Bukatar Ci Gaba Da Zama Hadaddiyar Kasa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version