ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton INEC Ya Nuna Machina Ne Dan Takarar Sanatan APC A Yobe Ta Arewa

by Sadiq
4 years ago
Machina

Wasu takardun Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), sun nuna cewa Hon. Bashir Machina ne ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a mazabar Yobe ta Arewa a Jihar Yobe.

Rahoton tawagar INEC da ta aika don sanya ido kan zaben fidda gwani da Omale Samuel, ya sanya wa hannu mai dauke da kwanan wata 28 ga Mayu, 2022, ya kuma nuna cewa Machina ya samu kuri’a 289 daga cikin kuri’a 300 da wakilan APC suka kada.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe
  • Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Har ila yau, wani rahoto daga ofishin INEC na jihar Yobe kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan majalisar dattawan Yobe ta Arewa, ya nuna cewa an gudanar da zaben ne a gidan gwamnati da ke Gashua, hedikwatar karamar hukumar Bade ta jihar.

ADVERTISEMENT

Gundumar ‘C’ ta kunshi kananan hukumomin Bade, Yusufari, Jakusko, Nguru, Karasuwa, da Machina.

Rahoton ya kara da cewa an fara zaben fidda gwanin da misalin karfe 11:30 na safe kamar yadda aka tsara, inda ya kara da cewa jami’an tsaro da jami’an zabe na kananan hukumomin da abin ya shafa duk sun halarta.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Yayin da za a fara zabukan fidda gwani, dukkan ’yan takara da dukkan jami’an jam’iyyar sun hallara domin sanya ido tare da kuma wakilan jam’iyyar.

“An fara zaben fidda gwani ne da bude addu’o’i daga sakataren kwamitin tsare-tsare Alh. Lawan Modu Sheriff,” in ji rahoton.

Tikitin takarar Sanata na APC a Yobe ta Arewa ya haifar da cece-kuce bayan da wanda ya lashe zaben, Bashir Machina, ya dage cewa ba zai bar takarar ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan ba, wanda a halin yanzu yake wakiltar kujerar sanatan.

Lawan dai ya tsaya takarar neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a farkon watan Yuni.

Sai dai shugabannin jam’iyyar APC na kasa sun mika sunan Lawan ga INEC domin tantance shi a matsayin dan takarar jam’iyyar a Yobe ta Arewa a zaben 2023, lamarin da ya janyo cece-ku-ce a shafukan sada zumunta.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.