ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton INEC Ya Nuna Machina Ne Dan Takarar Sanatan APC A Yobe Ta Arewa

by Sadiq
4 years ago
Machina

Wasu takardun Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), sun nuna cewa Hon. Bashir Machina ne ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a mazabar Yobe ta Arewa a Jihar Yobe.

Rahoton tawagar INEC da ta aika don sanya ido kan zaben fidda gwani da Omale Samuel, ya sanya wa hannu mai dauke da kwanan wata 28 ga Mayu, 2022, ya kuma nuna cewa Machina ya samu kuri’a 289 daga cikin kuri’a 300 da wakilan APC suka kada.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe
  • Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Har ila yau, wani rahoto daga ofishin INEC na jihar Yobe kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan majalisar dattawan Yobe ta Arewa, ya nuna cewa an gudanar da zaben ne a gidan gwamnati da ke Gashua, hedikwatar karamar hukumar Bade ta jihar.

ADVERTISEMENT

Gundumar ‘C’ ta kunshi kananan hukumomin Bade, Yusufari, Jakusko, Nguru, Karasuwa, da Machina.

Rahoton ya kara da cewa an fara zaben fidda gwanin da misalin karfe 11:30 na safe kamar yadda aka tsara, inda ya kara da cewa jami’an tsaro da jami’an zabe na kananan hukumomin da abin ya shafa duk sun halarta.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

“Yayin da za a fara zabukan fidda gwani, dukkan ’yan takara da dukkan jami’an jam’iyyar sun hallara domin sanya ido tare da kuma wakilan jam’iyyar.

“An fara zaben fidda gwani ne da bude addu’o’i daga sakataren kwamitin tsare-tsare Alh. Lawan Modu Sheriff,” in ji rahoton.

Tikitin takarar Sanata na APC a Yobe ta Arewa ya haifar da cece-kuce bayan da wanda ya lashe zaben, Bashir Machina, ya dage cewa ba zai bar takarar ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan ba, wanda a halin yanzu yake wakiltar kujerar sanatan.

Lawan dai ya tsaya takarar neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a farkon watan Yuni.

Sai dai shugabannin jam’iyyar APC na kasa sun mika sunan Lawan ga INEC domin tantance shi a matsayin dan takarar jam’iyyar a Yobe ta Arewa a zaben 2023, lamarin da ya janyo cece-ku-ce a shafukan sada zumunta.

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.