ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

by Abubakar Abba
1 week ago
Noma

Gwamnatin tarayya, ta nuna damuwarta kan yadda ake samun lalacewar kasar noma a fadin wannan kasa, inda ta bukaci a gagguta samar ingantattun sauye-sauye, domin bai wa kasar kariyar da ta kamata, musamman domin tabbatar da ganin an samu damar ci gaba da samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Karamin Ministan Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya yi wannan kira ne a Abuja wajen taron bikin ranar kasar noma ta wannan shekara da aka gudanar a Abuja, inda ya yi nuni da cewa; ta hanyar samar da ingantacciyar kasar noma, za a samu dorarren ci gaba da kuma samun wadataccen abinci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama
  • FAO Ta Horar Da Manoma 100 Kiwon Kifi A Kano

“Ingantacciyar kasar noma, na samar da amfanin gona da ya kai kashi 95 cikin 100, wanda kuma ‘yan kasar ke amfani da shi, sai dai ya bayyana cewa; kashi 33 cikin 100 na kasar noman, kusan duk ta zaizaye,” in ji Ministan.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, idan aka ce za a dawo da akalla kashi biyu zuwa uku na kasar noman, za a iya shafe nan da shekara 1000, ba a iya cimma hakan ba a wannan kasa.

Ministan ya kara da cewa, domin magance wannan matsala, ma’aikatar ta samar da wadataccen abinci tare da mayar da hankali kan bunkasa tsarin yin noma da suka hada da sauya yin noma zuwa wata gona da bai wa gandun dajin noma kulawar da ta kamata da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

“A watan da ya gabata, an kaddamar da shirin bai wa gonakin manoman kasar kulawar da ta kamata na kasa wato, NFSHS, wanda wasu manoma 600 da masu hadaka, suka samar da wajen da aka tsara na yin amfani da takin zamanin, domin kaucewa asarar da manoma ke yi da kuma yawan kashe kudade a wajen aikin noma.

“Shirin ya kuma hada da tanadar dakunan yin gwaje-gwajen kasar noma 774 da ke daukacin fadin kasar, wanda matasa da kuma mata ne za su tafiyar da su, tuni kuma an tanadi kayan aiki a jihohi 12 da ke kasar,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, Nijeriya ta kasance daya daga cikin kasashen da suka kulla yarjejiyar ta Afirka ta samar da takin zamani a 2024, wadda aka rattaba hannu, a kasar NAIROBI, musamman domin samar da ingantaccen takin zamani tare da hadaka da abokan hadaka kamar su GIZ, AGRA, IITA, bankin duniya, shirin sasakawa na Afrika da sauransu.

Ya bayyana cewa, ana kuma kan ci gaba da gudanar da aikin gwajin kasar noma, a jihohi 12 na kasar nan, kuma an sanya wannan aiki a cikin kasafin kudi na bana.

Sabi ya bukaci a mayar da hankali, domin bai wa kasar noma kariyar da ta kamata, musamman domin kare ta daga lalacewa, wanda hakan zai iya shafar kokarin da ake yi a kasar na samar da wadataccen abinci.

A jawabinsa a wajen taron, mataimakin shugaban cibiyar nazarin kimiyyar kasar noma (NISS), Olumuyiwa James Jayeoba, ya sanar da cewa; zai yi wuya a samu amfanin gona da ake bukata, matukar kasar noma na da matsala.

Yawan samun karuwar al’umma, na kara haddasa samun zaizaiyar kasa da kuma samun gurbatar muhalli.

Ya sanar da cewa, cibiyar ta NISS na kara kokari, wajen bai wa kasar noma kulawar da ta kamata, inda ya kara da cewa; ana kuma ci gaba da samar da sauye-sauyen bai wa kasar noma, kariyar da ta kamata a karkashin aikin na NFSHS, wanda ake gudanar da shi ta hanyar sabuwar hadaka.

Ya yi kira ga masu kirkiro da dokoki da masu safiyin kasa da sauran ‘yan kasar nan, da su rungumi tsarin mutunta kasar noma, musamman domin bai wa kasar noma kulawar da ta kamata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abubuwa Biyar Game Da Kiwon Talotalo
Noma Da Kiwo

An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani

December 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa
Noma Da Kiwo

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yaba Da Tsarin Aikin Noma Na Jihar Jigawa

December 19, 2025
Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman
Noma Da Kiwo

Kiwon Dabbobi Da Fasahar Kimiyyar Zaman

December 14, 2025
Next Post
NDLEA

NDLEA Ta Kama Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ga 'Yan Bindiga 'Gamboli' A Neja

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.