ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

by Abubakar Abba
7 months ago
Gwamnatin

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na son tara kimanin naira biliyan 160 a noman Alkama, a yayin noman rani na 2025 zuwa 2026.

Yunƙurin gwamnatin, na daga cikin ƙoƙarin da take ci gaba da yi na ƙarfafa samar da wadataccen abinci, musamaman domin rage dogaro da abincin da ake shigo wa da shi cikin ƙasar daga ƙetare.

Abubakar Kyari, Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, ya sanar da haka ne a Jere da ke Jihar Borno.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, Kyari ya sanar da hakan ne a yayin ƙaddamar da kayan aikin noma cikin rahusa, a ƙarƙashin shirin bunƙasa aikin noma na ƙasa (NAGS-AP).

  • Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano
  • Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani

Kyari ya ce, gwamnati ta keɓe kimin hekta 40,000 tare da yi wa manoman Alkama 80,000 a ɗaukacin faɗin ƙasar, domin wanzar da shirin, wanda ake sa ran za a samar da noman Alkama da aka ƙiyasta kuɗin zai kai, na Naira biliyan 160.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ya ƙara da cewa, Borno za ta bayar da gagarumar gudunmawa a ƙarƙashin shirin, duba da cewa; ta samar da hekta 3,000 tare kuma da yi wa manoman Alkama 6,000 rijista.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na da yaƙinin tara naira biliyan 160, duba da nasarar ta Alkama ƙarƙashin shirin ta yadda manoman Alkamar da aka taimakawa, suka samu 107,429 a kakar noma ta 2023 zuwa ta 2024, inda aka tara naira biliyan 474.6.

Ya ƙara da cewa, a kakar noma ta 2024 zuwa ta 2025, manoman Alkama 279,297 aka taimakawa, a ƙarƙashin shirin inda aka tara naira biliyan 893.7.

Kyari ya ci gaba da cewa, shirin na 2025 zuwa 2026; zai mayar da hankalin ne, wajen ƙara ƙarfafa samar da kayan aiki tare da kuma tabbatar da cewa, an samar wa da manoman Alkamar ingantaccen Irin Alkamar takin da takin zamani tare kuma  da cewa, kayan sun isa ga manoman.

Kazalika, Ministan ya sanar da cewa; za a tura Malaman aikin zuwa ɗaukacin faɗin ƙasar nan, musamman domin su koyar da manomanta na zamani.

Bugu da ƙari, a ƙarƙashin wannan shiri na NAGS-AP, za a faɗaɗa shi, zuwa jihohi 16 da suka haɗa da Adamawa, Bauchi, Borno, Kuros Riba, Gwambe, Kaduna, Kano, Kebbi, Neja, Filato, Sokoto, Taraba, Yobe da kuma  Zamfara.

Wannan ne karo na farko da aka sanya Jihar Kuros Riba a cikin wannan jerin jihohin.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yaba wa gwamnatin tarayya kan ci gaba da zuba jari a fannin  noman rani na Alkamar.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Abubuwan Da Suka Kamata Mata Su Sani Game Da Mazajensu (3) 

Abubuwan Da Suka Kamata Mata Su Sani Game Da Mazajensu (3) 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.