ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Tara Naira Biliyan 160 A Noman Alkama

by Abubakar Abba
7 months ago
Gwamnatin

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na son tara kimanin naira biliyan 160 a noman Alkama, a yayin noman rani na 2025 zuwa 2026.

Yunƙurin gwamnatin, na daga cikin ƙoƙarin da take ci gaba da yi na ƙarfafa samar da wadataccen abinci, musamaman domin rage dogaro da abincin da ake shigo wa da shi cikin ƙasar daga ƙetare.

Abubakar Kyari, Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, ya sanar da haka ne a Jere da ke Jihar Borno.

ADVERTISEMENT

A cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, Kyari ya sanar da hakan ne a yayin ƙaddamar da kayan aikin noma cikin rahusa, a ƙarƙashin shirin bunƙasa aikin noma na ƙasa (NAGS-AP).

  • Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano
  • Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani

Kyari ya ce, gwamnati ta keɓe kimin hekta 40,000 tare da yi wa manoman Alkama 80,000 a ɗaukacin faɗin ƙasar, domin wanzar da shirin, wanda ake sa ran za a samar da noman Alkama da aka ƙiyasta kuɗin zai kai, na Naira biliyan 160.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ya ƙara da cewa, Borno za ta bayar da gagarumar gudunmawa a ƙarƙashin shirin, duba da cewa; ta samar da hekta 3,000 tare kuma da yi wa manoman Alkama 6,000 rijista.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na da yaƙinin tara naira biliyan 160, duba da nasarar ta Alkama ƙarƙashin shirin ta yadda manoman Alkamar da aka taimakawa, suka samu 107,429 a kakar noma ta 2023 zuwa ta 2024, inda aka tara naira biliyan 474.6.

Ya ƙara da cewa, a kakar noma ta 2024 zuwa ta 2025, manoman Alkama 279,297 aka taimakawa, a ƙarƙashin shirin inda aka tara naira biliyan 893.7.

Kyari ya ci gaba da cewa, shirin na 2025 zuwa 2026; zai mayar da hankalin ne, wajen ƙara ƙarfafa samar da kayan aiki tare da kuma tabbatar da cewa, an samar wa da manoman Alkamar ingantaccen Irin Alkamar takin da takin zamani tare kuma  da cewa, kayan sun isa ga manoman.

Kazalika, Ministan ya sanar da cewa; za a tura Malaman aikin zuwa ɗaukacin faɗin ƙasar nan, musamman domin su koyar da manomanta na zamani.

Bugu da ƙari, a ƙarƙashin wannan shiri na NAGS-AP, za a faɗaɗa shi, zuwa jihohi 16 da suka haɗa da Adamawa, Bauchi, Borno, Kuros Riba, Gwambe, Kaduna, Kano, Kebbi, Neja, Filato, Sokoto, Taraba, Yobe da kuma  Zamfara.

Wannan ne karo na farko da aka sanya Jihar Kuros Riba a cikin wannan jerin jihohin.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yaba wa gwamnatin tarayya kan ci gaba da zuba jari a fannin  noman rani na Alkamar.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Abubuwan Da Suka Kamata Mata Su Sani Game Da Mazajensu (3) 

Abubuwan Da Suka Kamata Mata Su Sani Game Da Mazajensu (3) 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.