Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na son tara kimanin naira biliyan 160 a noman Alkama, a yayin noman rani na 2025 zuwa 2026.
Yunƙurin gwamnatin, na daga cikin ƙoƙarin da take ci gaba da yi na ƙarfafa samar da wadataccen abinci, musamaman domin rage dogaro da abincin da ake shigo wa da shi cikin ƙasar daga ƙetare.
Abubakar Kyari, Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, ya sanar da haka ne a Jere da ke Jihar Borno.
A cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, Kyari ya sanar da hakan ne a yayin ƙaddamar da kayan aikin noma cikin rahusa, a ƙarƙashin shirin bunƙasa aikin noma na ƙasa (NAGS-AP).
- Manoman Rake Sun Tabka Asarar Kimanin Naira Biliyan Biyu A Kano
- Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani
Kyari ya ce, gwamnati ta keɓe kimin hekta 40,000 tare da yi wa manoman Alkama 80,000 a ɗaukacin faɗin ƙasar, domin wanzar da shirin, wanda ake sa ran za a samar da noman Alkama da aka ƙiyasta kuɗin zai kai, na Naira biliyan 160.
Ya ƙara da cewa, Borno za ta bayar da gagarumar gudunmawa a ƙarƙashin shirin, duba da cewa; ta samar da hekta 3,000 tare kuma da yi wa manoman Alkama 6,000 rijista.
Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na da yaƙinin tara naira biliyan 160, duba da nasarar ta Alkama ƙarƙashin shirin ta yadda manoman Alkamar da aka taimakawa, suka samu 107,429 a kakar noma ta 2023 zuwa ta 2024, inda aka tara naira biliyan 474.6.
Ya ƙara da cewa, a kakar noma ta 2024 zuwa ta 2025, manoman Alkama 279,297 aka taimakawa, a ƙarƙashin shirin inda aka tara naira biliyan 893.7.
Kyari ya ci gaba da cewa, shirin na 2025 zuwa 2026; zai mayar da hankalin ne, wajen ƙara ƙarfafa samar da kayan aiki tare da kuma tabbatar da cewa, an samar wa da manoman Alkamar ingantaccen Irin Alkamar takin da takin zamani tare kuma da cewa, kayan sun isa ga manoman.
Kazalika, Ministan ya sanar da cewa; za a tura Malaman aikin zuwa ɗaukacin faɗin ƙasar nan, musamman domin su koyar da manomanta na zamani.
Bugu da ƙari, a ƙarƙashin wannan shiri na NAGS-AP, za a faɗaɗa shi, zuwa jihohi 16 da suka haɗa da Adamawa, Bauchi, Borno, Kuros Riba, Gwambe, Kaduna, Kano, Kebbi, Neja, Filato, Sokoto, Taraba, Yobe da kuma Zamfara.
Wannan ne karo na farko da aka sanya Jihar Kuros Riba a cikin wannan jerin jihohin.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yaba wa gwamnatin tarayya kan ci gaba da zuba jari a fannin noman rani na Alkamar.














