• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusa Majalisar Zartarwa: Shugabannin NNPP Sun Yi Wa Kwankwaso Tutsu

by Sulaiman
2 years ago
NNPP

Kungiyar shugabannin jam’iyyar NNPP na jihohi sun maka kwamitin gudanarwa na jam’iyyar a kotu kan rusa majalisar zartarwar jam’iyyar ba bisa ka’ida ba a jihohi 10 na tarayya.

Haka kuma Shugabannin sun zargi tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Injiniya Rabi’u Musa Kwakwaso na yin zagon kasa wanda hakan ya kawo wa jam’iyyar cikas wajen samun nasara a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Sun kuma yi ikirarin cewa Kwakwaso na yin yunkurin lalata tsarin jam’iyyar, inda suka yi zargin cewa yana amfani da ‘ya’yan jam’iyyar wajen aikata laifuka da kuma daukar matakin da bai dace ba.

Da zantawa da manema labarai a Ado Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, mai magana da yawun kungiyar shugabannin na kasa, Mista Dada Olayinka Olabode ya ce rusa shugabannin jihar da kananan hukumomi na jam’iyyar a jihohi 10 ya saba wa dokar jam’iyyar.

Dada wanda shi ne shugaban NNPP na Jihar Ekiti, ya kara da cewa shugabannin jam’iyyar da ‘ya’yan jam’iyyar na damar kalubalantar Kwakwaso a lokacin da suka fahimci yadda ake gudanar da abubuwa ba daidai ba, inda suka gayyace kwamitin ladabtarwa na uwar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Mun dauki matakin shari’a ne domin magance wannan rashin adalcin da aka yi wa mambobi sama da 7000 da suka shiga jam’iyyar a mazabu da kananan hukumomi da jihohi a Jihar Ekiti da kuma zababbun shugabannin jam’iyyar kusan 100,000 a fadin jihohi goma da wasu jihohi biyu da aka bayyana fitar da sanarwar korarsu.

“Kotun da ke Ado Ekiti ta bukaci wakilan uwar jam’iyyar su bayyana a gabanta a ranar 19 ga Satumba, 2023. Shari’ar tana gaban Mai Shari’a Aladejana na babban kotu ta 3 a da ke Jihar Ekiti”.

Kungiyar shugabannin jam’iyyar NNPP ta jihohi ta shawarci ‘yan Nijeriya, musamman ‘yan siyasa da su yi hattara da wadanda suke da alaka da jam’iyyar.

“Idan wani dan siyasa yana da sha’awar daidaitawa da jam’iyyarmu, akidarmu, falsafarmu, ya kamata ya gana da Cif Anibulam wanda shi ne uba kuma shugaban BoT na jam’iyyarmu”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Yi Murnar Sake Dawo Da Aikin Hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Zariya

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Murnar Sake Dawo Da Aikin Hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Zariya

LABARAI MASU NASABA

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.