ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusa Majalisar Zartarwa: Shugabannin NNPP Sun Yi Wa Kwankwaso Tutsu

by Sulaiman
3 years ago
NNPP

Kungiyar shugabannin jam’iyyar NNPP na jihohi sun maka kwamitin gudanarwa na jam’iyyar a kotu kan rusa majalisar zartarwar jam’iyyar ba bisa ka’ida ba a jihohi 10 na tarayya.

Haka kuma Shugabannin sun zargi tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Injiniya Rabi’u Musa Kwakwaso na yin zagon kasa wanda hakan ya kawo wa jam’iyyar cikas wajen samun nasara a zaben shugaban kasa na 2023.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Sun kuma yi ikirarin cewa Kwakwaso na yin yunkurin lalata tsarin jam’iyyar, inda suka yi zargin cewa yana amfani da ‘ya’yan jam’iyyar wajen aikata laifuka da kuma daukar matakin da bai dace ba.

ADVERTISEMENT

Da zantawa da manema labarai a Ado Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, mai magana da yawun kungiyar shugabannin na kasa, Mista Dada Olayinka Olabode ya ce rusa shugabannin jihar da kananan hukumomi na jam’iyyar a jihohi 10 ya saba wa dokar jam’iyyar.

Dada wanda shi ne shugaban NNPP na Jihar Ekiti, ya kara da cewa shugabannin jam’iyyar da ‘ya’yan jam’iyyar na damar kalubalantar Kwakwaso a lokacin da suka fahimci yadda ake gudanar da abubuwa ba daidai ba, inda suka gayyace kwamitin ladabtarwa na uwar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Mun dauki matakin shari’a ne domin magance wannan rashin adalcin da aka yi wa mambobi sama da 7000 da suka shiga jam’iyyar a mazabu da kananan hukumomi da jihohi a Jihar Ekiti da kuma zababbun shugabannin jam’iyyar kusan 100,000 a fadin jihohi goma da wasu jihohi biyu da aka bayyana fitar da sanarwar korarsu.

“Kotun da ke Ado Ekiti ta bukaci wakilan uwar jam’iyyar su bayyana a gabanta a ranar 19 ga Satumba, 2023. Shari’ar tana gaban Mai Shari’a Aladejana na babban kotu ta 3 a da ke Jihar Ekiti”.

Kungiyar shugabannin jam’iyyar NNPP ta jihohi ta shawarci ‘yan Nijeriya, musamman ‘yan siyasa da su yi hattara da wadanda suke da alaka da jam’iyyar.

“Idan wani dan siyasa yana da sha’awar daidaitawa da jam’iyyarmu, akidarmu, falsafarmu, ya kamata ya gana da Cif Anibulam wanda shi ne uba kuma shugaban BoT na jam’iyyarmu”.

NNPP
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

NNPP
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Yi Murnar Sake Dawo Da Aikin Hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Zariya

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Murnar Sake Dawo Da Aikin Hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Zariya

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.