• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushewar Gine-gine A Nijeriya: Ina Mafita?

byLeadership Hausa
1 year ago
Gine-gine

Babu wani lokaci da ya fi dacewa da a dauki matakin kawo karshen yadda gine-gine ke rushewa a sassan kasar nan fiye da wannan lokacin. A ‘yan watannin nan an samu rushewar gine-gine da suka kai ga rasa rayukan al’umma da dama da kuma asarar dukiya na miliyoyin nairori, har lamarin ya kai ga zama abin kunya ga Nijeriya a idon duniya.

Kwanakin baya ne wata makaranta a yankin Busi Buji da ke karamar hukumar Jos ta arewa a Jihar Filato ta rushe inda akalla dalibai 22 suka mutu wasu 132 suka ji munanan raunuka.

  • Matasa Sun Gudanar Da Zanga- zangar Lumana A Sakkwato
  • Wang Yi Ya Jaddada Muhimmancin Diflomasiyya Tsakanin Mabanbantan Al’ummu

Yawancin wadanda suka mutu da wadanda suka tsira, dalibai ne matasa masu zana jarrabawar zangon karshe ta kammala matakin karatun sakandire lokacin da ginin ya ruso a kansu. Abubuwa da dama aka dora wa laifin rushewar ginin sun kuma hada da rashin amfani da ingantattun kayan aiki da kuma kasancewar ginin yana kusa da rafi, an kuma kwashe kwana uku ana tafka ruwa, abin da ya haifar da ambaliyar ruwa a yankin.

Bayanai sun nuna cewa, kusan shekara 18 (2006) da suka wuce hukuma ta ba masu ginin wa’adin su gaggauta rusa ginin saboda an fahimci ba su yi amfani da ingantattun kayan aiki da suka kamata ba, amma suka yi biris da gargadin hukumar suka ci gaba da aikin ginin har zuwa wannan lokacin da ginin ya rushe.

A nata tsokacin, hukumar kula da harkokin injiniyoyi ta kasa (COREN) ta sanar da cewa a tsakanin watan Janairu zuwa watan Yulin 2024 an samu rushewar gine-gine 22 a fadin kasar nan wanda ya kai ga mutuwar mutum 33.

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

A taron manema labarai da shugaban kungiyar ta COREN, Sadik Abubakar, ya jagoranta, ya bayyana cewa, a cikin rushewar gine-gine da aka samu a fadin kasar nan, Jihar Legas na da kashi 27.27 yayin da Abuja da Anambara ke da kashi 18.18 na rushewar gine-gine da aka samu.

Ya kumka kara da cewa, Jihar Ekiti da Filato ke da kashi 9.09 kowannesu yayin kuma da Jihar Kano, Taraba da Neja ke da kashi 4.55 na yawan gidajen da suka rushe a cikin wannan shekarar.

Kididdiga ta kuma nuna cewa, Jihar Legas ce a kan gaba na yawan gidajen da suka rushe inda aka samu gidaje 91 wanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutum 354 tun daga shekarar 2012.

Haka kuma bayani ya nuna cewa, an samu rushewar gidaje 30 a yankin Abuja wanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutum 63 wasu kuma da dama suka ji raunuka daban-daban tun daga shekarar 1993.

A ‘yan shekarun nan, rushewar gine-gine ta zama ruwan dare inda ta baya-bayan nan ita ce wanda ta faru a ranar 12 ga watan Yuni na wani a gida kusa da makarantar ‘Dennis Memorial Grammar School (DMGS)’ a garin Onitsha, ta Jihar Anambara bayan wadda ta faru a ranar 13 ga wagan Yuni a Jihar Filato da kuma wadda ta faru a uguwar Kubwa ta yankin Abuja ranar 14 ga watan Yuli.

Wannan jaridar ta nuna mamakinta a kan yadda duk da asarar rayuka da ake samu sakamakon rushewar gine-ginen har yanzu gwamnati ba ta nuna damuwarta ba, ballantana ta kaddamar da dokar tabaci a bangaren.

A ra’ayinmu, za a iya kauce wa wadannan rushewar gine-ginen idan har gwamnati ta mayar da hankali wajen sanya ido a kan masu gine-gine. Haka kuma da masu gine-ginen sun mayar da hankali wajen amfani da ingantattun kayan aiki da hakan bai kai ga faruwa ba.

Amma kuma wani abin lura shi ne duk rashin kula da aiki na wasu jami’an gwamnati da kuma babakeren ‘yan kwangila masu aiki, zuwa yanzu babu wanda aka kama tare da yanke wa hukunci a kan laifin rushewar gini. Duk da mace-macen da ake yi babu wanda aka kama.

Daga dukkan alamu masu hannu da shuni ba sa fuskantar hukuncin laifin da suka tafka sakamakon rushewar gini a Nijeriya. Za a iya tunawa da rushewar cocin ‘Synagogue Church For All Nations’ da kuma ginin nan mai hawa 21 da ke layin Gerard a Ikoyi dukkan su a Jihar Legas.

Bayanin da ake da shi a halin yanzu yana nuna cewa, babu wanda aka hukunta sakamakon rushewar gini a duk fadin Nijeriya.

Muna cike da mamaki na yadda har yanzu gwamnati da masu ruwa da tsaki suka kawar da kai daga daukar matakai a kan wannan abin da ke faruwa a kan idon kowa da kowa, ana kuma asarar rayukan daruruwan mutane sakamakon rashin kula da ka’idoji da dokokin gine-gine.

Muna kira ga gwamnnanti da ta tabbatar da hukunta duk wani mai gini da ya yi sakaci da dokokin gine-gine har aka samu rushewar gini domin haka ya zama darasi ga sauran al’umma, ta haka za rage irin asarar rayuka da dukiyoyin al’umma da ake yi a kullum.

Ya kuma kamata a tabbatar da hukunta duk wani jami’in gwamnati da ya yi wasa da aikinsa har aka samu gini ya rushe in har ba a hukunta jami’an gwamnati masu kula da ingancin gine-gine ba to da wuya a kawo karshen wannan matsalar, za a kuma ci gaba da samun matsalar rushewar gine-ginen kenan a sassan kasar nan.

A kan haka ne shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bukaci gwamnonin jihohi su karfafa dokoki a jihohinsu domin kawo karshen rasa raywukan al’umma da ake samu sakamakon rushewar gine-gine fadin kasar nan musamman abin da ya faru a Jihar Filato kwanakin baya.

A yayin da muke goyon bayan kiraye-kirayen shugaban Majalisar Dattawa na a kawo karshen rushewar gine-gine, muna kira ga masu ruwa da tsaki a bangaren gine-gine su kara kaimi wajen sa ido a kan gine-gine da ake yi domin tabbatar da suna bin dokokin da aka tsara tare da kuma tabbatar an hukunta duk wanda ya saba wa doka, ta haka za a kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Yadda Muka Raba Tallafin Naira Biliyan 90 Ga Mahajjata -NAHCON

Yadda Muka Raba Tallafin Naira Biliyan 90 Ga Mahajjata -NAHCON

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version