ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Raba Tallafin Naira Biliyan 90 Ga Mahajjata -NAHCON

by Bello Hamza
2 years ago
NAHCON

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Nijeiya (NAHCON), Malam Jalal Ahmad Arabi, ya ce hukumar ta yi amfani da tallafin naira biliyan 90 da gwamnatin tarayya ta samu wajen cike gibin biyan kudin hajjin shekarar 2024 ga maniyyata.

Majalisar Wakilai ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin Hon. Sada Soli, daga Jihar Katsina domin binciko yadda hukumar ta gudanar da aikin hajji.

  • Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci
  • Wang Yi Ya Jaddada Muhimmancin Diflomasiyya Tsakanin Mabanbantan Al’ummu

Sai dai Arabi, a wani rahoto da ya fitar ya ce hukumarsa ta yi amfani da naira biliyan 90 wajen dinke barakar biyan kudin hajjin da ake bin maniyyata.

ADVERTISEMENT

“Gwamnatin Tarayya ta ba mu tallafin naira biliyan 90, wanda muka yi amfani da shi a tsanake wajen magance karin kudin aikin hajji da ba a taba yin irinsa ba.

“Yawan canjin dala ya sa farashin kowace kujera ya haura sama da naira miliyan 9, wanda hakan ya sa muka shiga tsakani don rage wa maniyyata nauyi.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

“Don magance matsalar, mun kira taro da wakilai daga jihohin kasar nan don tattaunawa kan lamarin. Sannan muka tattara jerin sunayen maniyyatan da suka rigaya suka biya naira miliyan 8 da aka amince da su.

“Daga baya, mun kara naira miliyan 1.3 ga mahajjata sama da 50,000 don kammala biyan su, wadanda muka tabbatar da cewa tafiyarsu ta hajji ba ta cika ba,” in ji shi.

Arabi ya bayyana cewa, a yayin da hukumar ta yi taka tsantsan wajen tafiyar da harkokin kudi tare da yin nazari a kan duk wani abin da aka kashe, ta tsaya tsayin daka wajen samar da ingantacciyar hidima ga alhazai, tare da yin wani kokari wajen tabbatar da jin dadi da walwalasu.

Ya ce ba kamar sauran kwamitocin da ke Nijeriya ba, NAHCON ba ta samun kudaden da gwamnatin tarayya ke karba akai-akai, ko dai a kowane wata ko a kowace shekara, domin samun kudaden gudanar da ayyukanta.

“Duk da cewa ba ta samun kaso na yau da kullum daga gwamnatin tarayya, na wata-wata ko na shekara, baya ga kason albashi, hukumar alhazai ta Nijeriya na kokarin isar da ayyuka na musamman ga kowa da kowa, tare da kara yawan albarkatunta don samar da mafi aiki da kyawun kwarewa,” in ji Arabi.

A jawabin da ya gabatar a babban taron ‘yan jarida na kasa da kasa a Abuja, Arabi ya bayyana cewa, ” A Dukkan shirye-shiryen da Hukumar NAHCON ta tabbatar da cewa hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki na da matukar muhimmanci.

Shugabanni da Manyan Sakatarori na Hukumar a jihohi (SPWBs) sun kasance wani bangare na kwamitin yanke shawara. Sun kuma taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da aikin hajjin bana cikin sauki. Hukumar ba ta taba yanke wani hukunci ba tare da tuntubar SPWBs da kuma ma’aikatan yawon shakatawa ba.

“Bayan da aka yi nasarar duba da kuma yin shawarwari kan yadda za a yi amfani da kudin hidima ga maniyyatan da ke shirin zuwa aikin hajjin shekarar 2024, adadin kudin aikin hajjin ya kai dala 5,692.25; ragi daga farashin hajji na 2023 na dala 6,401.31 kan farashin canjin naira 456.00.”

Yadda tsarin rabon ya kasance

Da farko, naira biliyan 90 da za ta biya kusan mahajjata 18,000 daga cikin mutum 50,000 da suka yi rajista a ranar 22 ga Maris, 2024. Daga baya, darajar ta fadi zuwa naira 1, 474.00 a watan Mayu 2024, hakan ya kawo jinkiri kan na watan Mayu 2024. Lissafin kamar yadda ake nufi da ragowa daga abin da alhazan da suka yi rajista za su cika.

Daga nan ne NAHCON ta samar da dabarun rabon kayan aiki wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin duk masu ruwa da tsaki a aikin hajjin 2024 sun ci gajiyar daidaiton kudi ta hanyar tallafin gwamnatin tarayya. An tallafa wa kowanne mahajjaci da naira 1,637,369.87 daga naira biliyan 90, iila mahajjata da ke karkashin shirin ceton aikin hajji (HSS).

Don haka, duk maniyyatan da suka yi rajista, in ban da na HSS, an bukaci su biya adadin naira 1,918,094.87 tun da naira biliyan 90 ba ta isa ta cika adadin ba. Sai dai an bukaci sabbin masu rajista da su biya naira miliyan 8, 454,464.74 da aka kebe daga gwamnatin tarayya. Ya bayyana cewa jami’ai da masu ruwa da tsaki daga kowane mataki na gwamnati sun ci gajiyar tallafin daga naira biliyan 90.

Ma’aikatan Yawon Shakatawa Masu Zaman Kansu (PTO):

Tun da farko, shugabannin PTO sun nuna aniyarsu ta neman wani mai ba da ayyuka ban da Ithra Al Khair. Ko da yake hukumar ba ta ki amincewa da hakan ba, NAHCON ta bukaci PTOs su sanar da ita matakin da suka dauka. A duk lokacin baje kolin aikin hajji da umrah, PTO na da ‘yancin yin bincike da tantance masu ba da ayyuka daban-daban ba tare da wani hani ba. To sai dai kuma a lokacin da shugabannin PTO karkashin kungiyar Alhazai da Umrah ta Nijeriya (AHUON) suka bayyana zabin da suka yi, sai suka gamu da rashin amincewa daga mambobinta.

 

PTO Da Tallafin Naira Biliyan 90:

AHUON ta aike da bukatar mambobinta suma su amfana da shiga tsakani na gwamnati tun da suma abin ya shafe su. Da farko dai, gwamnatin tarayya ta bukaci Hukumar NAHCON da ta bai wa maniyyatan da ke karkashin kason gwamnati fifiko a cikin tallafin naira biliyan 90, domin maniyyatan da ke karkashin wannan fanni su ne suka dade suna ajiye kudin aikin hajjinsu.

Abu na biyu, hukumar ta bayyana wa masu jirgin yawo (PTOs) cewa su ‘yan kasuwa ne da mata a fannin aikin hajji wadanda galibin abokan huldarsu daga masu hannu da shuni ne a cikin al’umma.

Don haka, hukumar kamar yadda aka ba da shawara ta tsaya tsayin daka kan cewa shiga tsakani na naira biliyan 90 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi, wani shiri ne da ya shafi mahajjata da ke karkashin kason gwamnati wadanda kudadensu ba su da karfi.

Alawus Na Matafiya (BTA):

Hukumar, bisa yarjejeniya da wakilan alhazai na jihohi, ta amince da biyan BTA na dala 500 ga kowane mahajjaci, a matsayin wani mataki na rage farashin kudin aikin hajji, duk mahajjaci mai bukatar karin dala ya samu tun da farashin ya kasance iri daya.

“Ku tabbatar da cewa NAHCON ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da gaskiya da rikon amana a dukkan al’amuranmu. Muna ci gaba da neman inganta hanyoyinmu don tabbatar da samun daidaiton damar yin amfani da kayan aiki da ayyuka ga dukkan mahajjata, ta yadda za mu tabbatar da tsarki da hadin kai na aikin hajji.

NAHCON
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Ba Zamu Lamunci Zanga-Zangar Tashin Hankali Ba – IGP 

Masu Zanga-Zanga Sun Ƙona Ofisoshin Ƴansanda, Sun Kashe Babban Jami'i

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.