Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Sanatoci Na Zargin Ma’aikatar Tsaro Da Aikata Cakwakiyar Kwangilar Miliyan N968.8

by Rabiu Ali Indabawa
December 31, 2020
in JAKAR MAGORI
2 min read
Sanatoci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mambobin Kwamitin Ba da Lamuni na Jama’a na Majalisar Dattawa sun nuna rashin gamsuwarsu ga wasu jami’an Ma’aikatar Tsaro da suka biya Naira 968.8m ga ’yan kwangila ba tare da amincewa ba. Rahoton na Babban jami’in binciken kudi na Tarayya, ya nuna wa ma’aikatan musamman biyan makudan kudade ga ’yan kwangilar. An yi shi ne don samarwa da kuma bayar da lambobin yabo don bikin tunawa da ranar samun ‘yancin kan Sojoji, amma ana zargin ba tare da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya da kuma Kwamitin bayar da kwangila na Minista ba.

Rahoton na AuGF ya tuhumi jami’an ma’aikatar tsaro da saukaka biyan kwangilolin duk da rashin amincewar da Mataimakin Darakta (Kasafin Kudi) ya gabatar a cikin wata takarda mai kwanan wata 24 ga Afrilu, 2013.

samndaads

Shugaban SPAC, Sanata Matthew Urhoghide, ya ci gaba da tambayar babban mai binciken saboda jami’an ma’aikatar tsaron sun kasa girmama gayyatar kwamitin don su bayyana bangarensu na zargin. Urhoghide ya lura da matukar damuwa cewa an gabatar da jerin gayyata ga ma’aikatar ba tare da wata amsa ba. Ya ce, saboda haka kwamitin ba shi da wata mafita face ya ci gaba da tambayar. AuGF ya ce an bayar da kwangilar ne a shekarar 2010, kuma an biya kashi 50 na kudin kwangilar ga ‘yan kwangilar yayin da aka biya ragowar kudin a ranar 26 ga Janairun 2015 ga dan kwangilar.

“An bayar da kwangilar samarwa da kuma bayar da lambobin yabo da kinti ribbons don bikin cikar ranar samun ‘yancin kan Sojojin Nijeriya a kan jimlar kwangilar da ta kai Naira miliyan 968,830,000.00. An biya duka kudin kwantiragin a watan Janairu. An biya Naira miliyan 484,415,000.00 a shekara ta 2010 wanda ke wakiltar kashi 50 cikin 100 na kwangilar kuma an biya ragowar Naira milyan 484,415,000.00 a ranar 26/01/2015 baitul malin kuɗi na lamba 4001.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Nasarawa Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin 2021

Next Post

Buhari Ya Bada Umarnin Hana Canjin Kudade Ga Masu Shigo Da Abinci

RelatedPosts

Huhunta

Kashin Kaza Ya Makale A Huhunta Shekara 14

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Wata mata ‘yar Kasar Sin mai shekara 22 da haihuwa...

Budurwarsa

Ya Kona Budurwarsa Saboda Ta Yanke Alakarsu

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Wata yarinya tana cikin halin ha'ula'i na rayuwarta bayan da...

Mari

Ya Kwashe Amaryarsa Da Mari A Taron Bikinsu

by Rabiu Ali Indabawa
3 days ago
0

Wani ango ya mari matar sa a gaban bakin da...

Next Post
Shigo Da Abinci

Buhari Ya Bada Umarnin Hana Canjin Kudade Ga Masu Shigo Da Abinci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version