Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Saukar Alkur’ani: Gwani Zangina Ya Yaba Wa Majalisar Mahaddata Alkur’ani

by Abdullahi Muhammad Sheka
February 2, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Saukar Alkur’ani: Gwani Zangina Ya Yaba Wa Majalisar Mahaddata Alkur’ani
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Majalisar Mahaddata Alkur’ani na babban birnin Tarayya Abuja Gwani Muhammad Zangina ya jinjinawa  Majalisar mahaddata Alkur’ani bisa karramawar da ta nuna wajen aika babbar tawaga karkashin Jagorancin Sakataren Majalisar na kasa Goni Sanusi Abubakar inda suka halarci daurin aure da Saukar Karatun ‘yayan  Gwani Zangina Wanda aka gudanar ranar Asabar a Kano.

Gwani Zangina yace  irin zumunci shi aka San halin Alkur’ani dashi, Kuma akansa muke har yanzu. Don Haka sai ya bukaci ‘yan uwa da kara jajircewa wajen gudanar da addu’o’i bisa halin da makarantun Allo suka tsinci Kai a Ciki, Gwani Zangina ya jawo ayoyi da hadisan Annabi domin hakurkurtar da ‘yan uwa bisa irin barazanar da wasu ke yiwa harkar makarantun tsangaya Wanda yace wannan duk lokacin ne.
Gwani Zangina ya godewa ‘yan uwa wadanda suka samu sukunin halartar wannan taro, dama wadanda addu’o’i suka Aiko duk muna godiya, a karshe ya yi fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
Goni Sunusi Abubakar Wanda ya wakilci Shugaban Majalisar mahaddata Alkur’ani na kasa Gwani Aliyu Saluhu Turaki ya bayyana cewa shugaban yaso kasancewa a wannan wuri domin ya san ahalullahi zasu hallara, Amma saboda abububawan da suka taru yasa Bai samu halartar wiring wannan Sauka ba, Amma zuciyarsa na tare damu a wannan wuri.
Goni Sunusi Abubakar ya isar da sakon shugaban na bukatar matsawa da addu’o’i domin fatan Allah ya Kawowa wannan kasa tamu karshen matsalolin taro da matsin tattalin arziki da ake fuskanta.
Shi ma mataimakin Shugaban Majalisar mahaddata Alkur’ani shiyyar Abuja Gwani Abdurrazak ya bayyana farin cikinsa bisa baiwar samun Alkur’ani da wadannan Yara biyar suka you, sannan ya yi addu’ar fatan samun zaman lafiya a auren da aka daura.

samndaads

 

SendShareTweetShare
Previous Post

An Cafke Wani Mutum Dauke Da Kati 17 Na ‘ATM’

Next Post

’Yan Bindiga Sun Kashe Wata Mai Sana’ar POS

RelatedPosts

Ummu-Kalthum Sambo

Tallan ’Ya’ya Mata Kalubale Ne Babba – Ummu-Kalthum Sambo

by Abdullahi Muhammad Sheka
21 hours ago
0

Daga Idris Umar,Zariya   A cikin makon daya gabacemu ne...

Ihiya'ussuna

Makarantar Ihiya’ussuna Ta Yi Sauka Karo Na Tara

by Abdullahi Muhammad Sheka
21 hours ago
0

Daga Idris Umar Zariya   Madarasatu ihiya'ussuna school of Arabic...

NARICT

NARICT: ’Yan Kungiyoyi Sun Yaba Wa Cigaban Da Farfesa Barminas Ke Samarwa A Zariya

by Abdullahi Muhammad Sheka
21 hours ago
0

Daga Idris Umar, Zariya   Mambobin kungiyoyin al'umma da ke...

Next Post
'Yan Bindiga Sun Kashe

’Yan Bindiga Sun Kashe Wata Mai Sana’ar POS

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version