• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Maka Dan Takarar Gwamnan APC Na Kano A Kotu

by Sadiq
3 years ago
Sha'aban

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Birni a Jihar Kano , Sha’aban Sharada, ya shigar da kara a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Kano, inda yake neman ta soke takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Gawuna, a matsayin dan takarar gwamna a 2023 na jam’iyyar APC a jihar.

Dan majalisar wanda ke wakiltar mazabar karamar hukumar Birni, ya bukaci kotun da ta soke zaben saboda zargin aikata rashin adalci yayin gudanar da zaben fidda-gwanin.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni
  • Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Duk da zabar Gawuna tare da tsohon kwamishinan kananan hukumomi Murtala Garo da wakilan jam’iyyar APC na Kano suka yi a matsayin ‘yan  takarar gwamna, Sharada bai gamsu da zaben ba.

Sha’aban na neman a soke zaben fidda gwanin da aka gudanar na zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar, inda ya ce an sabawa dokar zabe ta 2022.

A wata takardar karar da ya shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Kano, wanda ya shigar da karar ta hannun lauyansa J. O. Asoluka, SAN, ya ce zabar Gawuna ya sabawa sashe na 84 (1),(3),(8),(12). da (13) na dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Bugu da kari, lauyan wanda ya shigar da karar, inda ya bayyana cewa saba tanadin dokar da kuma ka’idojin jam’iyyar APC, gwamnatin jihar ta yi magudin zaben wakilai tare da tilasta musu zaben wanda ba su da ra’ayin zaba.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda zaben fidda gwanin ya gudana wanda ya bai wa masu rike da mukaman siyasa damar kada kuri’unsu duk da sashe na 84 (13) na dokar zabe wanda ya hana su shiga zaben fidda gwani.

A halin da ake ciki, mai shari’a Liman, ya bayar da izinin yin aiki da wasu kararraki biyu da mai shigar da kara ya gabatar.

Kotun ta dage sauraren karar daga kwanaki 30 zuwa kwanaki 15 domin a gaggauta sauraren shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.