ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Maka Dan Takarar Gwamnan APC Na Kano A Kotu

by Sadiq
4 years ago
Sha'aban

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Birni a Jihar Kano , Sha’aban Sharada, ya shigar da kara a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Kano, inda yake neman ta soke takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Gawuna, a matsayin dan takarar gwamna a 2023 na jam’iyyar APC a jihar.

Dan majalisar wanda ke wakiltar mazabar karamar hukumar Birni, ya bukaci kotun da ta soke zaben saboda zargin aikata rashin adalci yayin gudanar da zaben fidda-gwanin.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni
  • Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Duk da zabar Gawuna tare da tsohon kwamishinan kananan hukumomi Murtala Garo da wakilan jam’iyyar APC na Kano suka yi a matsayin ‘yan  takarar gwamna, Sharada bai gamsu da zaben ba.

ADVERTISEMENT

Sha’aban na neman a soke zaben fidda gwanin da aka gudanar na zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar, inda ya ce an sabawa dokar zabe ta 2022.

A wata takardar karar da ya shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Kano, wanda ya shigar da karar ta hannun lauyansa J. O. Asoluka, SAN, ya ce zabar Gawuna ya sabawa sashe na 84 (1),(3),(8),(12). da (13) na dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Bugu da kari, lauyan wanda ya shigar da karar, inda ya bayyana cewa saba tanadin dokar da kuma ka’idojin jam’iyyar APC, gwamnatin jihar ta yi magudin zaben wakilai tare da tilasta musu zaben wanda ba su da ra’ayin zaba.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda zaben fidda gwanin ya gudana wanda ya bai wa masu rike da mukaman siyasa damar kada kuri’unsu duk da sashe na 84 (13) na dokar zabe wanda ya hana su shiga zaben fidda gwani.

A halin da ake ciki, mai shari’a Liman, ya bayar da izinin yin aiki da wasu kararraki biyu da mai shigar da kara ya gabatar.

Kotun ta dage sauraren karar daga kwanaki 30 zuwa kwanaki 15 domin a gaggauta sauraren shari’ar.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.