ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Maka Dan Takarar Gwamnan APC Na Kano A Kotu

by Sadiq
4 years ago
Sha'aban

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Birni a Jihar Kano , Sha’aban Sharada, ya shigar da kara a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Kano, inda yake neman ta soke takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Gawuna, a matsayin dan takarar gwamna a 2023 na jam’iyyar APC a jihar.

Dan majalisar wanda ke wakiltar mazabar karamar hukumar Birni, ya bukaci kotun da ta soke zaben saboda zargin aikata rashin adalci yayin gudanar da zaben fidda-gwanin.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni
  • Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Duk da zabar Gawuna tare da tsohon kwamishinan kananan hukumomi Murtala Garo da wakilan jam’iyyar APC na Kano suka yi a matsayin ‘yan  takarar gwamna, Sharada bai gamsu da zaben ba.

ADVERTISEMENT

Sha’aban na neman a soke zaben fidda gwanin da aka gudanar na zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar, inda ya ce an sabawa dokar zabe ta 2022.

A wata takardar karar da ya shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Kano, wanda ya shigar da karar ta hannun lauyansa J. O. Asoluka, SAN, ya ce zabar Gawuna ya sabawa sashe na 84 (1),(3),(8),(12). da (13) na dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Bugu da kari, lauyan wanda ya shigar da karar, inda ya bayyana cewa saba tanadin dokar da kuma ka’idojin jam’iyyar APC, gwamnatin jihar ta yi magudin zaben wakilai tare da tilasta musu zaben wanda ba su da ra’ayin zaba.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda zaben fidda gwanin ya gudana wanda ya bai wa masu rike da mukaman siyasa damar kada kuri’unsu duk da sashe na 84 (13) na dokar zabe wanda ya hana su shiga zaben fidda gwani.

A halin da ake ciki, mai shari’a Liman, ya bayar da izinin yin aiki da wasu kararraki biyu da mai shigar da kara ya gabatar.

Kotun ta dage sauraren karar daga kwanaki 30 zuwa kwanaki 15 domin a gaggauta sauraren shari’ar.

MASU ALAKA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.