ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Qatar

Tuni dai shirye-shiryen gasar cin kofin duniya ta yi nisa kuma sani wace kasa ce za ta kara da wata a gasar Kofin Duniya na wannan shekarar bayan kammala wasannin neman shiga gasar a Qatar da aka yi a birnin Doha na Qatar.

Gasar wadda za a fara a watan Nuwamba mai zuwa, za ta zama ta farko da za a gudanar a nahiyar Gabas ta Tsakiya kuma ta farko a irin wannan
lokacin na shekara duk da cewa matakin da aka dauka na zabar Katar ya tayar da jijiyoyin wuya.

  • Manchester United Za Ta Yi Da-na-sanin Rabuwa Da Ni, Cewar Pogba

Za a buga wasannin matakan karshe daga ranar 21 ga watan Nuwamba zuwa 18 ga watan Dasamba – lokacin da yanayin zafi ke kai wa 25C a ma’aunin celcius a kasar ta Katar, lamarin da masana suke ganin za’a iya samun tsananin zafi duk da haka.

ADVERTISEMENT

Da a ce za a buga wasannin a tsakanin Yuni zuwa Yuli, kamar yadda aka saba, za a buga su ne cikin tsananin zafin da ke kai wa fiye da maki 40C, har zuwa maki 50C duk da cewa tun farko Katar ta nemi ta gudanar da gasar a lokacin bazara kuma a rufaffun dakunan wasa masu na’urar sanyaya wuri, amma daga baya sai aka watsar da batun.

Watannin Nuwamba da Disamba cike suke da hada-hada a gasar kasashen Turai ta kungiyoyi kuma ‘yan wasa da yawa za su amsa kira domin buga wa kasashensu wasannin Kofin Duniya a Katar na 2022.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

A gefe guda kuma, gasar kasashe kamar Premier League na Ingila, da La Liga ta Sifaniya, da Serie A ta Italiya, za su dakatar da wasanni mako daya kafin fara gasar sai an kammala gasar za su ci gaba da nasu wassannin.

A shekarar 2010 ne Katar ta yi nasarar samun damar karbar bakuncin gasar ta hanyar lashe zaben da FIFA ta shirya tsakanin mambobinta guda 22. Ta doke kasashen Amurka da Japan da Australia, kuma ita ce kasar Larabawa ta farko da za ta karbi bakuncin gasar.

An zargi Katar da bai wa jami’an tsaro cin hancin Dala miliyan uku da dubu 700 domin samun damar, amma an wanke ta bayan gudanar shekara biyu ana bincike kuma shugaban FIFA na wancan lokacin, Sepp Blatter, ya goyi bayan bukatar Katar a lokacin, amma ya ce da alama FIFA ta yi kuskure.

Yanzu haka Mista Blatter na fuskantar shari’a a kotu a Switzerland bisa zargin zamba da almubazzaranci da sauran tuhumar cin hanci da rashawa tare da abokinsa, tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta kasashen turai, Michael Platini.

Sannan kungiyoyin kare hakki na Amnesty International da Human Rights Watch na zargin Katar da take hakkin ma’aikata ‘yan kasar waje da ke aikin gina filayen wasannin gasar ta cin kofin duniya.

Tun shekara uku da suka gabata aka fara wasannin neman shiga Kofin Duniya kuma kasar Faransa mai rike da kofin a shekara ta 2018, ta tsallake, amma Italiya mai rike da kofin gasar Turai ba ta samu gurbi ba.

A wasannin karshe na cancantar shiga gasar da aka buga, an raba tawagogin kasashe 32 zuwa rukunin tawaga hudu. Tawagogin da suka fito daga nahiya daya an raba su da juna – ban da kasashen Turai, inda ake iya hada kasa biyu a rukuni daya.

Sannan kasashen Brazil da Ingila da Sifaniya na cikin kasashen da ake sa ran za su cinye gasar, kuma ana iya sayen giya ne a manyan otel-otel kawai na Katar, matakin da shima abin dubawa ne musamman ga kasashen da ake shan giya. Katar mai yawan al’umma miliyan 2.9 na daya daga cikin kasashe mafiya arziki a duniya saboda arzikin man fetur da gas da take da su, kuma ta gina sabbin filayen wasa bakwai kawai saboda gasar, da kuma wani sabon birni da za a buga wasan karshe a cikinsa.

Ana gina sabbin otel sama da 100, da sabuwar tashar jirgin kasa da wasu tituna, har ila yau kwamatin shirya gasar ya yi kiyasin cewa ana sa ran mutum miliyan daya da rabi ne za su halarci gasar.

Kamar yadda muka sani kasar Katar ta Musulmi ce mai bin addini sau da kafa saboda haka aka gargadi magoya baya da su kasance masu da’a saboda akwai dokokin hana shan giya kuma ana iya saya ne a manyan otel-otel kawai. Kofi daya na giya kan kai Dala 13 – kwatankwacin Naira dubu biyar, amma kuma masu shirya gasar sun ce za a iya sayar da giyar a wasu kebantattun wurare na ‘yan kallon gasar.

Kungiyoyin kare hakkin ‘yan luwadi da madigo na ta kiran gwamnatocin kasashensu da su tabbatar musu da kariya, yayin da wasu ‘yan kallo daga Wales suka ce za su kaurace wa gasar bayan kasarsu ta samu gurbi.

Masu gasar Kofin Duniyar sun ba da amsa cewa ana maraba da kowa, amma Katar ba za ta sassauta dokokinta ba kan luwadi da madigo, matakin da ake ganin kamar wani tarnaki ne ga kasashen da suka halarta hakan.

Qatar
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Yadda FIFA Ta Yi Yunƙurin Sasanta Rikicin Israila Da Amurka A Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Yi Yunkurin Arcewa Bayan Daba Wa Mai Ciki Wuka Ta Mutu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.