ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Argentina Za Ta Sake Lashe Kofin Duniya Saboda Rashin Zuwan Nijeriya?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 weeks ago
Argentina

Tawagar ‘yan wasan Nijeriya ta Super Eagles ba ta samu tikitin zuwa gasar cin kofin duniya ba da za a yi a Amurka da Mexico da kuma Canada a shekara ta 2026 mai kamawa.

Hakan ya biyo bayan da Jamhuriyar Congo ta fitar da ita a wasan karshe a cike gurbi daga yankin Afirka da ci 4-3 a bugun fenariti, bayan da tun farko suka tashi 1-1 bayan minti 120.

  • Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa ‘Yan Aiki Aure Mazajensu
  • Yadda Za Ki Kara Wa Kanki Tsawon Gashi

Nijeriya ta kai wasan karshe bayan doke Gabon 4-1 ranar Alhamis, yayin da Jamhuriyar Congo ta fitar da Kamaru a dai ranar., sakamakon da ya ba su damar karawa a tsakaninsu a daren ranar Lahadi a kasar Moroco.

ADVERTISEMENT

Yanzu haka Jamhuriyar Congo za ta hadu da wasu tawagogi shida daga wasu nahiyoyin a cikin watan Maris a Mexico, domin fitar da biyun da za su cike gurbin shiga wasannin da kasashe 48 za su fafata.

Wasu na cewa Argentina ce za ta sake lashe kofin duniya a badi, bayan da Super Eagles ta kasa kai bantenta. Sai dai hakan ba ya nufin tawagar Nijeriya tana takawa Argentina birki idan sun hadu.

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

Tawagar ‘yan wasan kasar Argentina mai rike da kofin duniya da ta lashe a Katar a 2022 tana daga fitattun da ke wakiltar wasannin a koda yaushe, wadda jimilla tana da uku a tarihi.

Wannan shi ne karon farko da Nijeriya ta kasa samun tikitin shiga gasar cin kofin duniya karo biyu a jere a tarihi tun bayan da ta fara halartar wasannin a shekarar 1994, wadda karo uku tana kai wa zagaye na biyu a wasannin.

Kenan Super Eagles, wadda ta buga gasar kofin duniya sau shida daga tara baya, ba ta je wasannin da aka yi a 2006 da 2022 da 2022 ba, ga kuma yanzu ba za ta yi karawar 2026 ba.

Argentina ta lashe kofin duniya a 1978 da kuma 1986 a lokacin da Nijeriya ba ta fara zuwa wasannin ba, sannan Argentina ta dauki kofi na uku a 2022 da aka yi a Katar, gasar da Super Eagles ba ta samu tikitin shiga ba.

Daga gasa 18 da Argentina ta halarci gasar cin kofin duniya ta yi ta biyu a 1930 da 1990 da kuma 2014, haka kuma ta yi nasarar cin wasa 47 daga wasa 88 da ta buga a babbar gasar kwallon kafar ta duniya.

Hakan ne ya sa wasu ke cewa Argentina ce za ta sake daukar kofin na duniya a badi, saboda Super Eagles ba ta samu tikitin shiga wasannin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey
Wasanni

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

December 20, 2025
FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

December 17, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Ƙaryata Zargin Kutsen 'Yan Ta'addan Boko Haram A Jihar Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.