• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

Abiola Issah ita ce matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya. A shekarar 2013, ta shiga shirin bayar da horo da kamfanin CCECC na kasar Sin ya shirya game da guraben aikin yi da za a samar ga al’ummar Nijeriya wajen gudanar da layin dogo na birnin Abuja, wanda kamfanin ya dauki nauyin ginawa. Bayan tsawon shekaru biyar, Abiola ta zama matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya, har ma tsohon shugaban kasar marigayi Muhammadu Buhari ya gana da ita. Abiola ta ce, kamar sauran mutane irinta da dama, wannan layin dogo ya canja rayuwarta, ta ce, “sufuri ya zama tushen ci gaban kasa. Hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin a fannin sufuri, ba kawai ya inganta ababen more rayuwar kasashen ba, ya kuma farfado da tattalin arzikinsu da kuma samar da guraben ayyuka ga al’ummarsu. Matasa irina mun koyi fasahohi har ma mun samu ayyukan yi.”

 

Abin da ya faru ga malama Abiola kyakkyawan misali ne da ya shaida yadda ci gaban kasa ya taimaka ga inganta hakkin dan Adam, wato manyan ababen more rayuwa sun sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin kasa, tare da samar da guraben ayyukan yi ga al’ummarta, kuma ta hakan an kyautata rayuwar al’umma, baya ga karewa da inganta hakkin dan Adam.

 

Ke nan hakkin rayuwa da kuma hakkin ci gaba sun kasance na farko daga cikin hakkokin dan Adam. Idan babu ci gaban kasa, babu tushen sauran hakkokin dan Adam ke nan. A don haka ne, a gun taron kara wa juna sani tsakanin Sin da kasashen Afirka kan hakkin dan Adam karo na farko da aka gudanar kwanan baya a birnin Addis Ababa, mahalarta taron sama da 200 da suka zo daga kasashen Sin da Afirka kimanin 44, suka yi musayar ra’ayoyi game da batun “hakkin samun ci gaba”. Matsayar da aka cimma a wajen taron ta kuma yi nuni da cewa, ci gaban kasa tushe ne na warware dukkanin matsalolin hakkin dan Adam.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

 

A hakika, kwarewar kasar Sin a fannin inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa, tana da muhimmiyar ma’ana ga kasashen Afirka wajen fid da kansu daga kangin talauci da kuma tabbatar da hakkin dan Adam. A game da hakan, Prof. Melha Rout Biel, shehun malami a cibiyar nazarin tsare-tsare da manufofi ta kasar Sudan ta Kudu ya yi nuni da cewa, “Kasashen Afirka da Sin dukkansu sun taba fuskantar koma baya sakamakon katsalandan da wasu kasashen suka yi musu. Batun hakkin ci gaba da kasar Sin ke magana a kai, abu ne da ya faru gare mu, don haka, muke goyon bayan kasar Sin wajen kokarin tabbatar da hakkinmu na ci gaba.”

 

Har kullum, kasar Sin na dukufa a kan “inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa”, ta kuma gabatar da shawarar raya kasashen duniya, don “kar a bar wata kasa a baya”, kuma ta hanyar inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a wannan fannin tare da cimma kyawawan nasarori. Misali kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararru na kasashen Afirka, don inganta kwarewar kasashen wajen tabbatar da ci gabansu. A kwanan nan, layin dogon Mombasa zuwa Nairobi da kamfanin kasar Sin ya gina ya cika kwanaki 3000 da fara aiki, wanda ya rage kudaden jigilar kayayyaki kimanin kaso 40% ga al’ummar wurin, tare da samar musu guraben aikin yi dubu 74, kuma hakan ya tabbatar da hakkin ci gaban al’ummar kasar. Har wa yau, Kasar Sin ta kuma yi gine-ginen ababen samar da makamashi mai tsabta sama da 100 a Afirka, ciki har da tashar samar da lantarki daga karfin ruwa ta Zungeru, wadanda suka samar da karfi ga kasashen Afirka wajen tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

 

Duk da haka, kasashen yamma sun sha yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin makami wajen tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe masu tasowa. A Afirka, kasashen yamma su kan bayar da gudummawar tattalin arziki bisa gindaya sharuda kan batutuwan hakkin dan Adam, sai dai irin katsalandan da suke yi ta fakewa da batun hakkin dan Adam kan haifar da munanan illoli ga kare hakkin dan Adam a kasashen Afirka. Don haka, a matsayar da aka cimma a gun taron, Sin da kasashen Afirka sun jaddada cewa, suna goyon bayan kasa da kasa su zabi hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki, kuma suna masu adawa da siyasantar da batun hakkin dan Adam ko kuma mai da shi tamkar makami.

 

A yayin da malama Abiola Issah ke samun horo a kasar Sin, ta taba shiga jirgin kasa mai saurin tafiya na kasar. Ta ce ba ta taba ganin jirgi mai sauri haka ba, kuma fatan ta shi ne, wata rana Nijeriya ma ta samu irin jirgin, kuma ta zama matukiya ta farko ta irin wannan jirgin kasa a gida Nijeriya. A ganina, yayin da ake aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da tabbatar da sakamakon da aka cimma a gun taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, burinta zai cika nan bada jimawa ba, kuma Sin da kasashen Afirka za su tabbatar da ci gabansu na bai daya bisa hadin gwiwarsu, a yayin da za su dada kyautata rayuwar al’ummunsu da kuma kara inganta hakkin dan Adam bisa ci gaban kasashensu.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
Ra'ayi Riga

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Tinubu
Ra'ayinmu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Sin
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Next Post
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.