Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin na adawa da duk wani aikin musgunawa ko haifar da illa a mashigin tekun Hormuz.
Guo ya bayyana haka ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da ya jagoranta a Yau Talata, yayin da yake amsa tambaya game ta datse wani jirgin ruwan dakon kaya na kasar waje da ya fito daga babban yankin kasar Sin, da Amurka ta yi a mashigin tekun Hormuz kwanan nan.
Bugu da kari, Guo ya sanar da cewa, ministan harkokin wajen Sin Wang Yi zai kai ziyarar aiki kasashen Cambodia da Thailand da Myanmar bisa gayyatar da aka yi masa.
Ban da haka kuma, dangane da hadayar da firaministar Japan Takaichi Sanae ta gabatar a wurin ibada na Yasukuni, wanda aka sadaukar ga wadanda suka aikata laifukan yaki a yakin duniya na biyu, Guo ya bayyana cewa Sin tana adawa sosai kuma ta yi Allah wadai da mummunan aikin da Japan ta yi game da wurin ibadar. (Safiyah Ma)















Discussion about this post