Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian, ya ce, dangane da babban taron fasahar AI na duniya da taron manyan jami’ai na duniya kan tafiyar da sha’anin fasahar AI da za a gudanar a birnin Shanghai gobe Jumma’a, Sin za ta yi amfani da wannan taron a matsayin wata dama ta yin musayar ra’ayi da cimma matsaya daya da dukkan bangarori, da kuma tabbatar da cewa fa’idodin zamani na fasaha sun kawo karin alheri ga kasashe masu tasowa, wanda hakan zai ba da damar ci gaban fasaha don inganta samun bunkasa da wadatar al’ummar dan Adam.
Lin ya bayyana haka ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Alhamis.Dangane da rahoton da Asusun Demokuradiyya na Kasa na Amurka wato NED ya fitar kuwa, inda aka yayata “ra’ayin barazanar Sin”, Lin ya ce Sin ta bukaci wasu cibiyoyi da mutane na Amurka da su sauya karkataccen ra’ayinsu mara dacewa game da Sin.Bugu da kari, game da shawarar da gwamnatin Papua New Guinea ta yanke ta rufe “Ofishin kula da harkokin tattalin arziki na Taipei dake Papua New Guinea,” Lin ya ce wannan ya sake nuna cewa bin ka’idar kasar Sin daya tak a duniya shi ne abin da al’ummar duniya baki daya ta amince da shi.
Ban da haka kuma, Lin ya bayyana cewa, wasu kafafen yada labarai na kasashen yamma, sun gabatar da sabon ra’ayin da ake kira “tsarin nuna biyayya” a cikin sharhi kan manufofin harkokin wajen kasar Sin, inda ya ce wannan ra’ayi ya yi hannun riga da gaskiyar lamarin musayar ra’ayoyi da hadin gwiwar da Sin ke yi da kasashen Asiya da ma na duniya.(Safiyah Ma)














