Jam’iyyar (ADC) ta sake shiga cikin rikicin cikin gida bayan daya daga cikin fitattun jagororinta, Salihu Mohammed Lukman, ya sanar da dakatar da kasancewarsa a jam’iyyar da kuma gamayyar jam’iyyun adawa, inda ya zargi tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da haddasa wulakanci da ware shi daga harkokin jam’iyyar.
A cikin wata sanarwa da ya aikewa Shugaban ADC na kasa, Sanata David Mark, tare da kwafin ga shugabannin gamayyar adawa, Lukman ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bayan watanni na abin da ya kira ci gaba da cin zarafinsa da kuma nuna masa wariya daga El-Rufai da wasu na kusa da shi kan yadda ake tafiyar da harkokin jam’iyyar a Jihar Kaduna.
Lukman ya ce ya yi hakuri na tsawon lokaci, amma ya kasa ci gaba da jure irin yadda ake mu’amala da shi.
Ya ce, “Ina matukar bakin ciki da wannan mataki, amma ba zan iya ci gaba da jure irin wulakancin da nake fuskanta daga wasu shugabannin Kaduna ba, musamman Malam Nasir El-Rufai.”
Ya kuma yi zargin cewa ana karkatar da yanke hukunci kan wakilcin shugabanci a Kaduna domin a mayar da shi saniyar ware, yana mai cewa an rage darajarsa duk da irin kokarin da ya yi wajen kafa da hada kan gamayyar jam’iyyun adawa.
Tsohon Mataimakin Shugaban APC na shiyyar Arewa maso Yamma ya bayyana cewa ya shafe sama da shekara guda yana kokarin sasanta shugabannin adawa a Kaduna tare da gina ADC, amma a maimakon a yaba masa sai aka mayar da shi abin hari.
Lukman ya ce saboda hakan ya yanke shawarar dakatar da kasancewarsa a ADC da kuma gamayyar jam’iyyun adawa, yana mai cewa gara ya dakata da harkokin siyasa na wani lokaci fiye da ci gaba da bin abin da ya kira “burin da ya rushe.”
Har ila yau, ya zargi wasu shugabannin gamayyar da rashin bin ka’idojin dimokuradiyya, yana mai cewa suna maimaita irin salon siyasar da suka dade suna suka, wanda ya janyo matsaloli a jam’iyyunsu na baya.
Lukman ya yi zargin cewa tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, na tuntubar wasu mutane a Kaduna da, a cewarsa, ba su da cikakkiyar niyyar gina ADC, tare da yin watsi da wadanda suka sadaukar da lokacinsu wajen karfafa jam’iyyar.













