Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika wa Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, takardar tabbatar da shi a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na shekarar 2027, kwanaki kadan bayan jam’iyyar APC ta tabbatar da sunansa a tikitin jam’iyyar.
An bayyana hakan ne cikin wani bidiyo da Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Kafafen Sada Zumunta, Olusegun Dada, ya wallafa a ranar Alhamis.
Bidiyon ya nuna lokacin da Shettima ya isa wajen taron, inda ya yi gajeriyar ganawa da Shugaba Tinubu kafin shugaban ya mika masa takardar da ke tabbatar da nadinsa a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2027.
Yayin wallafa bidiyon, Dada ya rubuta cewa, “Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika wa Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, takardar tabbatar da shi a matsayin abokin takararsa a zaben 2027.”













