ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

by Sulaiman
40 minutes ago
Amurka

Sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran a ’yan kwanakin nan ya ja hankalin al’ummun duniya baki daya, tare da hasashen sake dandana mummunan tasirin da yakin zai haifar ga daukacin duniya baki daya idan har ya tsawaita. Duniya na fatan Amurka da Iran za su koma teburin shawarwari ba tare da bata lokaci ba, kana za su kai ga aiwatar da matakan dakatar da zubar da jini cikin hanzari, tare da taka wa yakin birki baki daya. 

Kasa da wata guda da cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Amurka da Iran, a yanzu tashin hankalin na sake farfadowa. Mun dai ga yadda tun da sanyin safiyar ranar Talata, Amurka ta fara kaddamar da sabbin hare-hare kan sassan Iran cikin kwanaki uku a jere, yayin da ita ma Iran ke mayar da martani kan cibiyoyin aikin soji na Amurka dake kasashen yankinta.  

Sakamakon wannan dauki ba dadi, tuni farashin mai ya fara hauhawa, kura ta turnuke a mashigin Hormuz, kuma tsarin sufurin hajojin kasuwanci da ya yi matukar rauni a sakamakon tashin hankalin da ya gabata, a yanzu ma ya sake shiga yanayi na ha’ula’i. Masana da dama na cewa, Amurka da Iran ba za su mori wata fa’ida ba daga sake barkewar tashin hankali, kuma dukkanin kasashen duniya za su dandana kudarsu sakamakon sake barkewar tashin hankalin da ake gani a yanzu. 

ADVERTISEMENT

Kafin cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin sassan biyu, mun ga yadda aka kai ruwa rana wajen tattaunawa, da tuntuba, da shiga tsakani na wasu sassa, har dai aka kai lokacin da Amurka da Iran suka sanar da kawo karshen yaki, da dakatar da daukacin ayyukan soji daga dukkanin fannoni, da kaucewa amfani da karfin soji ta kowane bangare. Sassan biyu sun kuma sha alwashin mutunta ikon mulkin kai da tsaron yankunan juna, tare da kaucewa tsoma hannu cikin harkokin gidan juna.  

Yanzu haka dai tasirin sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran ya jefa farashin mai cikin yanayi na rashin tabbas, tare da sake gurgunta hada-hadar sufurin hajoji ta mashigin Hormuz, kuma hasashen baya bayan nan na asusun IMF ma, dangane da karuwar ci gaban tattalin arzikin duniya na bana ya ragu da kaso 0.1 bisa dari, kasa da na watan Afirilun da ya shude, inda IMF din ya alakanta hakan kai tsaye da rikicin na gabas ta tsakiya. 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Alal hakika, duniya ba za ta yi farin ciki da dawowar yaki ba. Kuma sassan kasa da kasa na fatan sassan da rikicin ya shafa za su gaggauta komawa teburin shawarwari, maimakon dauki ba dadi da zai haifar da illa ga dukkanin bangarori. (Saminu Alhassan) 

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Sulaiman
    Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

MASU ALAKA

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Next Post
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.