ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

by Sulaiman
2 months ago
Amurka

Sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran a ’yan kwanakin nan ya ja hankalin al’ummun duniya baki daya, tare da hasashen sake dandana mummunan tasirin da yakin zai haifar ga daukacin duniya baki daya idan har ya tsawaita. Duniya na fatan Amurka da Iran za su koma teburin shawarwari ba tare da bata lokaci ba, kana za su kai ga aiwatar da matakan dakatar da zubar da jini cikin hanzari, tare da taka wa yakin birki baki daya. 

Kasa da wata guda da cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Amurka da Iran, a yanzu tashin hankalin na sake farfadowa. Mun dai ga yadda tun da sanyin safiyar ranar Talata, Amurka ta fara kaddamar da sabbin hare-hare kan sassan Iran cikin kwanaki uku a jere, yayin da ita ma Iran ke mayar da martani kan cibiyoyin aikin soji na Amurka dake kasashen yankinta.  

Sakamakon wannan dauki ba dadi, tuni farashin mai ya fara hauhawa, kura ta turnuke a mashigin Hormuz, kuma tsarin sufurin hajojin kasuwanci da ya yi matukar rauni a sakamakon tashin hankalin da ya gabata, a yanzu ma ya sake shiga yanayi na ha’ula’i. Masana da dama na cewa, Amurka da Iran ba za su mori wata fa’ida ba daga sake barkewar tashin hankali, kuma dukkanin kasashen duniya za su dandana kudarsu sakamakon sake barkewar tashin hankalin da ake gani a yanzu. 

ADVERTISEMENT

Kafin cimma yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin sassan biyu, mun ga yadda aka kai ruwa rana wajen tattaunawa, da tuntuba, da shiga tsakani na wasu sassa, har dai aka kai lokacin da Amurka da Iran suka sanar da kawo karshen yaki, da dakatar da daukacin ayyukan soji daga dukkanin fannoni, da kaucewa amfani da karfin soji ta kowane bangare. Sassan biyu sun kuma sha alwashin mutunta ikon mulkin kai da tsaron yankunan juna, tare da kaucewa tsoma hannu cikin harkokin gidan juna.  

Yanzu haka dai tasirin sake barkewar hare-hare tsakanin Amurka da Iran ya jefa farashin mai cikin yanayi na rashin tabbas, tare da sake gurgunta hada-hadar sufurin hajoji ta mashigin Hormuz, kuma hasashen baya bayan nan na asusun IMF ma, dangane da karuwar ci gaban tattalin arzikin duniya na bana ya ragu da kaso 0.1 bisa dari, kasa da na watan Afirilun da ya shude, inda IMF din ya alakanta hakan kai tsaye da rikicin na gabas ta tsakiya. 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Alal hakika, duniya ba za ta yi farin ciki da dawowar yaki ba. Kuma sassan kasa da kasa na fatan sassan da rikicin ya shafa za su gaggauta komawa teburin shawarwari, maimakon dauki ba dadi da zai haifar da illa ga dukkanin bangarori. (Saminu Alhassan) 

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.