ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago

Bankin Duniya ya bayyana damuwa kan yadda kashi 79 cikin 100 na ƴan Nijeriya har yanzu ke rayuwa cikin talauci ko kuma ke cikin haɗarin faɗawa cikin talauci duk da sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin tarayya ta ke aiwatarwa kusan shekaru uku da suka gabata.

Bankin ya ce samar da ayyukan yi shi ne babbar hanyar da za ta fitar da miliyoyin ƴan Nijeriya daga ƙangin talauci, kamar yadda ya bayyana a cikin Tsarin Haɗin Gwuiwa da Nijeriya (Country Partnership Framework – CPF) na 2026 zuwa 2032.

Rahoton ya nuna cewa kashi 33 cikin 100 na ƴan Nijeriya na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato ba sa iya biyan mafi ƙarancin buƙatun abinci, yayin da kashi 61 cikin 100 ke rayuwa ƙasa da layin talauci na ƙasa da aka shata.

ADVERTISEMENT

Bankin ya ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a Nijeriya, musamman a jihohi Arewa.

Rahoton ya kuma bayyana cewa sama da mutane miliyan 86 ba su da wutar lantarki, yayin da matasa tsakanin miliyan uku zuwa huɗu ke kai wa matsayin fara neman aiki a kowace shekara ba tare da isassun damar samun aikin yi ba.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Bankin Duniya ya amince cewa wasu sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar, ciki har da cire tallafin fetur, da sassauta tsarin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje, da tsaurara manufofin kuɗi da sauye-sauyen haraji, sun taimaka wajen daidaita tattalin arziƙi da ƙara amincewar masu zuba jari.

Rahoton ya ce bunƙasar tattalin arziƙin ƙasar ta ƙaru daga kashi 3.5 cikin 100 a farkon rabin shekarar 2024 zuwa kashi 3.9 cikin 100 a daidai wannan lokaci na shekarar 2025, Yayin da ajiyar kuɗaɗen waje ta haura dala biliyan 42.

Sai dai Bankin ya gargaɗi cewa hauhawar farashin kayayyaki na ci gaba da rage ƙarfin sayen al’umma, musamman masu ƙaramin ƙarfi, yayin da shirye-shiryen tallafin jin daɗin jama’a ke tafiya a hankali.

Haka kuma, ya ce raunin hukumomi, da rashin ingantaccen haɗin gwuiwa wajen aiwatar da manufofi da ƙarancin gaskiya wajen tafiyar da kasafin kuɗi na daga cikin manyan ƙalubalen da ke iya hana tattalin arziƙin Nijeriya samun cikakkiyar farfaɗowa.

Bankin ya jaddada cewa ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziƙi tare da ƙarin gyare-gyaren tsari zai zama wajibi domin inganta rayuwar ƴan Nijeriya a nan gaba.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.