Bankin Duniya ya bayyana damuwa kan yadda kashi 79 cikin 100 na ƴan Nijeriya har yanzu ke rayuwa cikin talauci ko kuma ke cikin haɗarin faɗawa cikin talauci duk da sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin tarayya ta ke aiwatarwa kusan shekaru uku da suka gabata.
Bankin ya ce samar da ayyukan yi shi ne babbar hanyar da za ta fitar da miliyoyin ƴan Nijeriya daga ƙangin talauci, kamar yadda ya bayyana a cikin Tsarin Haɗin Gwuiwa da Nijeriya (Country Partnership Framework – CPF) na 2026 zuwa 2032.
Rahoton ya nuna cewa kashi 33 cikin 100 na ƴan Nijeriya na rayuwa cikin matsanancin talauci, wato ba sa iya biyan mafi ƙarancin buƙatun abinci, yayin da kashi 61 cikin 100 ke rayuwa ƙasa da layin talauci na ƙasa da aka shata.
Bankin ya ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a Nijeriya, musamman a jihohi Arewa.
Rahoton ya kuma bayyana cewa sama da mutane miliyan 86 ba su da wutar lantarki, yayin da matasa tsakanin miliyan uku zuwa huɗu ke kai wa matsayin fara neman aiki a kowace shekara ba tare da isassun damar samun aikin yi ba.
Bankin Duniya ya amince cewa wasu sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar, ciki har da cire tallafin fetur, da sassauta tsarin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje, da tsaurara manufofin kuɗi da sauye-sauyen haraji, sun taimaka wajen daidaita tattalin arziƙi da ƙara amincewar masu zuba jari.
Rahoton ya ce bunƙasar tattalin arziƙin ƙasar ta ƙaru daga kashi 3.5 cikin 100 a farkon rabin shekarar 2024 zuwa kashi 3.9 cikin 100 a daidai wannan lokaci na shekarar 2025, Yayin da ajiyar kuɗaɗen waje ta haura dala biliyan 42.
Sai dai Bankin ya gargaɗi cewa hauhawar farashin kayayyaki na ci gaba da rage ƙarfin sayen al’umma, musamman masu ƙaramin ƙarfi, yayin da shirye-shiryen tallafin jin daɗin jama’a ke tafiya a hankali.
Haka kuma, ya ce raunin hukumomi, da rashin ingantaccen haɗin gwuiwa wajen aiwatar da manufofi da ƙarancin gaskiya wajen tafiyar da kasafin kuɗi na daga cikin manyan ƙalubalen da ke iya hana tattalin arziƙin Nijeriya samun cikakkiyar farfaɗowa.
Bankin ya jaddada cewa ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziƙi tare da ƙarin gyare-gyaren tsari zai zama wajibi domin inganta rayuwar ƴan Nijeriya a nan gaba.













