ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani A Fannin Saukaka Tsadar Lantarki A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Tuni kasar Sin ta yi nasarar kafa managarcin tsarin samarwa da cinikayyar lantarki daga hanyoyi mabanbanta. Kasar Sin ta wuce gaba a matsayin jagora a fannin samar da lantarki daga hasken rana, da karfin iska, da ma fasahohin da ake amfani da su a ababen hawa masu aiki da lantarki da ma adana lantarkin, wanda hakan ya sanya ta zama jigo a fannin sauyi zuwa amfani da makamashi marar gurbata yanayi.

Wasu alkaluma da hukumar kasa da kasa mai lura da makamashi da ake iya sabuntawa ta fitar a baya bayan nan, sun nun yadda aka samu raguwar tsadar makamashin lantarki a duniya baki daya, musamman wanda ake samarwa daga hasken rana da iska, lamarin da ake alakantawa da babbar gudunmawar kasar Sin.

Bisa manufofinta, Sin ta yi matukar kokari wajen saukaka farashin makamashi mai tsafta ga dukkanin sassan duniya. Daya daga cikin misalai kan hakan shi ne shirin “Zirin lantarki ta hasken rana na Afirka”, wato muhimmiyar manufar hadin gwiwa ta kasashe masu tasowa dake da nufin shawo kan sauyin yanayi, wadda aka kaddamar a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT

Karkashin shirin, Sin ta sanya hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da kasashe irinsu Burundi da Chadi a nahiyar Afirka, domin hade fifikon masana’antunta da yalwar hasken rana na sassan Afirka, ta yadda hakan zai taimakawa al’ummun nahiyar Afirka samun lantarki mai dorewa.

Tuni wannan hadin gwiwa tsakanin kamfanonin Sin da na kasashen Afirka, ya samar da lantarki ta hasken rana da ya zarce jimillar gigawatts 1.5.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

A daya bangaren kuma, kasar Sin ta yi namijin kokari wajen ingiza manufar rage fitar da hayakin carbon mai dumama yanayi tsakanin kasashen duniya.

Ana iya ganin wannan kwazo na kasar Sin daga yadda a shekarar 2024 kadai, ta fitar da tarin kayayyaki masu kunshe da fasahohin makamashi mai tsafta, wadanda aka tabbatar sun taimaka wajen rage fitar da hayakin cabon a wajen kasar, da kaso daya bisa dari cikin na jimillar kasashen duniya.

Masharhanta dai na ganin domin cimma burin da ake fata, kamata ya yi sassan kasa da kasa su kara fadada cudanya da juna, a fannin sauya akala zuwa nau’o’in makamashi marasa dumama yanayi, su yaukaka musayar fasahohi da tsare-tsare a fannin, tare da karfafa matakan cin gajiyar fasahohin kasar Sin na samarwa, da amfana daga makamashi mai tsafta, ta yadda hakan zai amfani daukacin sassan duniya baki daya.

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • Sulaiman
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • Sulaiman
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
Daga Birnin Sin

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Next Post
Rashin Tsaro: Jihar Kwara Ta Rufe Makarantu A Ƙananan Hukumomi 4

Rashin Tsaro: Jihar Kwara Ta Rufe Makarantu A Ƙananan Hukumomi 4

LABARAI MASU NASABA

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.