Kungiyar ‘Yan Kasuwar Arewa wato ‘Arewa Traders Association’ da haxin gwiwar bankin Ja’iz da Taj Bank, sun gudanar da babban taro domin wayar da ‘yan kungiyar gami da tallafa musu ta yadda za su bunqasa kasuwancinsu ta hanyar koya musu kasuwanci a zamanance da suka hada fasahar zamani dabaru.
Da yake jawabi a wurin taron, shugaban qungiyar Arewa Traders Association na kasa, Alhaji Adamu Hassan Ibrahim, cewa ya yi “Maqasudin wannan taro shi ne, a kara jawo ‘yan uwansu ‘yan kasuwa su fahimci sabon tsarin na kasuwanci wanda duniya take tafiya da shi, a ilimantar da kananan ‘yan kasuwa, ka san an ce ka ba wa mutum ilimin abu ya fi ka ba shi abin hannunka, saboda mu muke jama’a a Arewa sannan mu muke da abin da muka gada iyaye da kakanni na kasuwancin nan, to kasusancin nan ba ya yiwywa sai akwai tsarin zamani saboda rayuwa ta canja, wannan shi ne dalilin da ya sa muka shirya wannan taro na ilmantar da juna.
Shi kuwa shugaban kasuwar Deidei, cewa ya yi ‘Na farko dai yaya za su yi gudanar da harkokin kasuwancinsu ta hanyar adana bayanai, da kuma hanyoyin sadarwa. Kyakkyawar mu’amala na sanyawa mutum ya samu kwastotmomi, sannan sanin sanin ya za a yi ka habaka kasuwancinka, ya ta yaya za a yi ka shiga bankuna ka samu jari, wae irin tallafi bankuna ke bayarwa, wane irin tallafi su bayarwa na Inshora? Da uaran abubuwa marasa dadi da suke samun ‘yan kasuwa kamar su gobara rikice-rikice ko hadura, to wane tsari muke da shi na Inshora da idan wannan abu ya faru ga ‘yan kasuwarmu su kawo mana dauki? Wannan ya sa muka yi hadin gwiwa da Ja’iz da Taj Bank su zo domin samun mafita,” in ji shi.
Tun da fari a jawabin da ya gabatar Manajan Daraktan Ja’iz Takafu Alhaji Ibrahin Shehu, yaba wa wadanda suka shirya taron ya yi. Baya ga haka ya bayyana cewa shi aikinsa ya nuna wa mutum wata hanya da zai bi ya kaucewa asara a kasuwanci idan kuma aka samu asarar to a nuna masa yadda zai bi ya maye gurbin abin da ya rasa ta hanyar tanadi a bankinsu, domin babu yadda za a yi ka fara kasuwanci ba ka samu a sara ba. A karshe ya ce za su samu lokaci domin yi wa mambobi cikakke bayanin yadda lamarin yake.
Shima wakilin kamfanin Dangote Hashim Cewa ya yi, duk wanda zai yi kasuwanci to kada ya yi haka kai tsaye kamar yadda wasu ke yi, ya ce yana da kyau mutum ya san daga ina ya faro sannan kuma ina ya nufa. “Yawancin mutanenmu na Arewa da mutum ya fara kasuwanci ya fara samun kudi shi ke nan sai sayen mota sayen gida kara aure, sai ka ga ba a je ko ina ba ‘yana so ya zama wane kuma idan ka ga mutum ya zama wane to ta irin haka bane, in ji shi.
Sai kuma wakiliyar bangaren abin da ya shafi bunkasawa da karfafa kwazon ayyuka na kasa wadda Omoyili ta wakilci wanda ya kamata ya zo bai sai samu ikon zuwa ba, wacce ta magana akan kyakkyawar kulawa akan muhimmancin bunkasa kasuwanci domin kasuwanci shima abu ne mai rai wanda ke da hanyoyi da matakai da ake bi na ganin cewa an bunkasa shi.
Ta ja hankalin ‘yan kasuwa kan ba wa kwastomomi muhimmanci domin idan babu su kasuwanci ba zai inganta ba, don haka a cewarta ya zama wajibi ya kasance kana da kyakkyawar mu’amala da su.
Shugabannin kungiyar na jihohin Arewa ga mambobinta ne dai suka samu halartar wannan muhimmin.














