ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta ce dakarun sojin Nijeriya sun gano gawarwaki biyu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe su.

Samuel Aruwan, kwamishinan ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta Jihar Kaduna, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya kuma tabbatar da cewa sojojin sun kwato wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su tare da lalata sansanonin ‘yan bindiga a dazuzzukan Chikun-Kachia-Kajuru.

  • Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka
  • Talauci Ne Ke Sa Wasu ‘Yan Nijeriya Yin Barace-Barace A Kasashen Waje —Shugaban NAHCON

A cewarsa, bayanan da rundunar ta samu ta nuna cewa sojojin sun yi artabu da ‘yan bindiga a kewayen Kwanti, karamar hukumar Chikun, inda ya kara da cewa ‘yan bindigar sun tsere zuwa cikin dajin, sun bar babura hudu da sojojin suka kwato.

ADVERTISEMENT

Ya ce sojojin sun gano wasu maza biyu da aka yi garkuwa da su, Muntaka Abubakar da Nwabueze John, inda ya ce sun kuma gano tare da kwashe gawarwakin wasu mata biyu da ‘yan bindigar suka kashe.

Ya ce wadanda aka ceto sun sake haduwa da iyalansu, bayan an kai agajin farko ga daya daga cikinsu da ya samu raunuka.

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Ya kara da cewa, wata tsohuwa mai suna Tabawa Laraba, mai shekaru 85, sojojin sun ceto ta a yankin Kuzo, inda aka duba ta tare da yi mata bayani kafin ta sake haduwa da iyalanta.

“Sojojin sun kara sintiri zuwa yankunan Abrom, Gabachuwa da kuma dajin Kujeni da suka hada da kananan hukumomin Kajuru, Chikun da Kachia,” in ji shi.

Ya ce a yayin da sojojin ke artabu da ‘yan bindigar da suka tsere zuwa cikin daji, inda suka kakkabe sansanoninsu, sannan suka kwato bindigu kirar AK-47 guda biyu tare da wayoyin hannu guda uku, kakin sojoji da kayayyakin hada bama-bamai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa
Manyan Labarai

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
Next Post
Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.