ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

by Sadiq
4 years ago
Sojoji

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta ce dakarun sojin Nijeriya sun gano gawarwaki biyu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe su.

Samuel Aruwan, kwamishinan ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta Jihar Kaduna, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya kuma tabbatar da cewa sojojin sun kwato wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su tare da lalata sansanonin ‘yan bindiga a dazuzzukan Chikun-Kachia-Kajuru.

  • Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka
  • Talauci Ne Ke Sa Wasu ‘Yan Nijeriya Yin Barace-Barace A Kasashen Waje —Shugaban NAHCON

A cewarsa, bayanan da rundunar ta samu ta nuna cewa sojojin sun yi artabu da ‘yan bindiga a kewayen Kwanti, karamar hukumar Chikun, inda ya kara da cewa ‘yan bindigar sun tsere zuwa cikin dajin, sun bar babura hudu da sojojin suka kwato.

ADVERTISEMENT

Ya ce sojojin sun gano wasu maza biyu da aka yi garkuwa da su, Muntaka Abubakar da Nwabueze John, inda ya ce sun kuma gano tare da kwashe gawarwakin wasu mata biyu da ‘yan bindigar suka kashe.

Ya ce wadanda aka ceto sun sake haduwa da iyalansu, bayan an kai agajin farko ga daya daga cikinsu da ya samu raunuka.

LABARAI MASU NASABA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

Ya kara da cewa, wata tsohuwa mai suna Tabawa Laraba, mai shekaru 85, sojojin sun ceto ta a yankin Kuzo, inda aka duba ta tare da yi mata bayani kafin ta sake haduwa da iyalanta.

“Sojojin sun kara sintiri zuwa yankunan Abrom, Gabachuwa da kuma dajin Kujeni da suka hada da kananan hukumomin Kajuru, Chikun da Kachia,” in ji shi.

Ya ce a yayin da sojojin ke artabu da ‘yan bindigar da suka tsere zuwa cikin daji, inda suka kakkabe sansanoninsu, sannan suka kwato bindigu kirar AK-47 guda biyu tare da wayoyin hannu guda uku, kakin sojoji da kayayyakin hada bama-bamai.

MASU ALAKA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Next Post
Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.