Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Tagomashin Da Kasuwar Baje Kolin Duniya Ta Kaduna Za Ta Samu A Bana

by
4 months ago
in LABARAI
2 min read
Kasuwar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT
  • Za Mu Tabbatar Da Cikakken Tsaro —KADCIMMA

| Daga Bello Hamza,

An bayyana cewa, kasuwar baje kolin duniya ta Kaduna da za a ci a bana za ta samu karin tagomashi fiye da na baya sosai bisa kwararowar kasashen waje da sauran manyan ‘yan kasuwa na duniya. Har ila yau an nunar da cewa an kammala dukkan shirye-shirye musamman a kan abn day a shafi bangaren samar da tsaro don ganin an samu nasarar gudanar da bikin baje kolin masa’anantu da aka saba yi duk shekara a filin baje koli da ke Rigachikum Kaduna.

Babban Darakta na Majalisar ‘yan Kasuwa, Masa’anatu da Albakun Gona (KADCCIMA) na Jihar Kaduna, Alhaji Usman Garba Saulawa bayyana haka a tattanawarsa da Wakilimu jim kadan bayan shugabannin majalisar suka kawo wa Kamfanin Jaridar Leadership Hausa ziyara a babban ofishinta dake Abuja ranar Laraba.

Labarai Masu Nasaba

Wata Mata Ta Sha Da Kyar Bayan An Kama Ta Da Zargin Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Bauchi

Ministar Kudi Ta Yaba Wa Gwamnatin Kano Bisa Gudummawarta Ga Ma’aikatarta

Ya kuma kara da cewa, Majalisar Masa’anantun na da dogon tarihi da kamfanin Jaridar Leadership, “Ta yadda suke tallata tare da yayata harkokinmu, musamman a wannan karon da muke shirin gabatar da kasuwar baje koli na duniya karo na 43 a nan Kaduna daga ranar 25 ga watan Fabrairu zuwa 6 ga watan Maris 2022, muna bukatar kamfanin Leadership ta taimake mu wajen yayata harkokin da za mu gabatar kafin taron da yayin gudanar da taron kuma ta bamu shawarwari bayan taron don gyara tare da kara azama a shirin mu na shekaru masu zuwa” in ji shi.

Babban Daraktan ya kuma sanar da cewa, zuwa yanzu sun samu nuna sha’awar shiga shirin daga kasashe na duniya da dama kamar su Moroko, Masar, Insland, Birtaniya da wasu kasashe a nahiyar Asiya, yayin da kuma zuwa yanzu jihohi da dama da kamfanoni masu zaman kansu da masu zuba jari daga ciki da kuma kasashen waje sun bayyana aniyarsu na shiga taron baje kolin, wanda shi ne mafi shahara a Nijeriya.

Ya kuma bayyana cewa, a wannan karon an tanadi wasu shirye-shirye masu kayatarwa, da suka hada da kacici tsakanin ‘yan makarantu, za kuma a bayar da kyaututtuka ga wadanda suka nuna bajinta. Daga nan ya kuma bayyana cewa, sun yi cikakken shiri a bangaren tsaro don ganin an gudanar da biki cikin nasara, “Kwamitin tsaro a karkashin shugabancin Kanal Jibrin Hassan (Sarkin Yakin Hadeja) ya yi dukkan shiri na ganin an samar da issashen jami’an tsaro don ganin ba a samu wani barazana ba kafin da yayin gudanar da taron” in ji shi.

Daga nan ya ce, suna samun dukkan goyon baya daga gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Malam Nasiru El-Rufa’i. Cikin tawagar da suka kawo ziyarar akwai Alhaji Sulaiman Aliyu, Alhaji Faruk Sukaiman da Kanal Jibrin Hassan (Sarkin Yakin Hadejia).

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Nijeriya Na Bukatar Albasa Tan Miliyan 2.5 Duk Shekara – Shugaban ‘Yan Albasa Na Kaduna

Next Post

Ba Ma Goyon Bayan Kafa Dokar Haramta Yajin Aiki

Labarai Masu Nasaba

Wata Mata Ta Sha Da Kyar Bayan An Kama Ta Da Zargin Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Bauchi

Wata Mata Ta Sha Da Kyar Bayan An Kama Ta Da Zargin Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
9 mins ago
0

...

Nijeriya

Ministar Kudi Ta Yaba Wa Gwamnatin Kano Bisa Gudummawarta Ga Ma’aikatarta

by Mustapha Ibrahim
41 mins ago
0

...

Kungiyar Agaji Ta Kasar Saudiyya Ta Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 131 Ga Marayu A Kebbi

Kungiyar Agaji Ta Kasar Saudiyya Ta Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 131 Ga Marayu A Kebbi

by Umar Faruk
13 hours ago
0

...

Nijeriya Na Bukatar Shugaban Da Kasar Ce Kawai A Gabansa —Obasanjo

Nijeriya Na Bukatar Shugaban Da Kasar Ce Kawai A Gabansa —Obasanjo

by
15 hours ago
0

...

Next Post
Ba Ma Goyon Bayan Kafa Dokar Haramta Yajin Aiki

Ba Ma Goyon Bayan Kafa Dokar Haramta Yajin Aiki

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: