• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Takaitaccen Nazari A Kan Yadda Ake Noman Karas A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Ko shakka babu, ana yin noman Karas yadda ya kamata a Nijeriya, sannan ya kasance kayan lambu na biyu a duniya da aka sani baya ga Dankali, kazalika kuma yana daukar daga kimanin kwana 70 zuwa 80 kafin ya fara nuna.

Haka zalika, Jihar Filato ce a kan gaba wajen nomansa a duk fadin wannan kasa, sakamakon yanayi da jihar ke da shi mai matukar kyau wanda ya da ce da nomansa.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Yadda Ake Nomawa

Ana samun nau’ikan Irinsa da dama a Nijeriya, wadanda suke samar da amfanin gona mai tarin yawa, wasu daga cikin nau’ikan Irin da ake kira a turance sun hada da ‘Danbers, Chantanay, Nantes, Armsterdam’ da sauran makamantansu, wadanda kuma sun kasance suna bukatar ingattaciyar kasar noma.

Ganin cewa, Irinsa na da wuyar sha’ani yana kuma son kulawar da ta dace, ya zama wajibi a gyara gonar don shuka Irin yadda ya dace, haka nan; ya fi dacewa a shuka Irin a kan Kunyoyi yadda jijiyoyinsa za su samu sukunin shiga cikin kasar da aka shuka shi.

Amfanin Karas:

Yana da matukar amfani sosai ga rayuwar Dan Adam, domin kuwa ana yin amfani da shi wajen hada miya ko abinci tare da sarrafa shi zuwa kayan zaki, haka nan yana dauke da wasu sinadaran hada magunguna  da suka hada da ‘thiamine da riboflabin’.

Har ila ya, cin sa tsura na taimakawa wajen kara lafiyar jikin  dan Adam tare da da dai-daita sinadarin ‘cholesterol’ da ke rage kiba a jikin mutum.

Bugu da kari, yana dauke da sinadarin ‘beta carotene, bitamins A, D, C, E, K, potassium da kuma minerals’, wadanda suke taimaka wa wajen karin gani na Ido tare da kara gyara fatar jiki.

Har ila yau, Karas na dauke da sauran sinadaran da ke kara wa Dan Adam karfin jiki da wadanda suka hada da: ‘fat, protein, carbohydrates, sodium, zinc, phosphorus, potassium, manganese, calcium and iron’.

Yawan ruwan da ke jikinsa, ya kan kai  kashi 88 a cikin 100, wanda yake dauke da sindarin ‘protein da ya kai kimanin kashi 0.9 a cikin dari, sai kuma sinadarin ‘fibre’ da ya kai kashi 2.8 a cikin dari, inda sinadarin ‘fat’ ke dauke da kashi 0.2 a cikin dari, sai kuma sinadarin ‘carbohydrates’ da kashi 9 cikin dari.

Canjin Yanayi:

Karas ya fi son yanayi mai sanyi, musamman wanda ya kai  ma’unin yanayi daga 16 zuwa 20, amma ma’aunin yanayin da ya wuce 28, na rage masa saurin girma kuma idan aka shuka Irin yana kaiwa daga kimanin kwana bakwai zuwa 21 kafin ya fara fitowa daga cikin kasa.

Yadda Ake Shuka Shi:

Bayan an tona kasa an zuba Irin a yayin shuka shi, ana rufe shi ne a hankali, kazalika wasu manoman kan yi wa gonar da za su shuka shi ban ruwa har zuwa tsawon awa ashirin da hudu kafin su shuka Irin, musamman don ya samu danshi sosai. Sannan, ana kuma bukatar manomi ya nemi shawarar masana a kan wannan Iri da kuma Takin da ya dace ya yi amfani da shi.

Har ila yau, za a iya zuba Takin Gargajiya; bayan wata guda da shuka shi, domin amfanin ya yi saurin girma.

Ban Ruwa:

Karas na bukatar yawan ruwa, musamman a lokacin noman rani, don ya girma da wuri; kana kuma ana so bayan an shuka shi a tabbatar da an yi masa ban ruwa, domin ya kasance yana dauke da danshi.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Girbin Karas:

Ana girbe shi ne, bayan an tabbatar da cewa ya gama girma yadda ya kamata, sannan manomi zai iya barin sa a gona ba tare da ya girbe shi ba, sai dai kuma ana bayar da shawara cewa; ka da a bar shi ya jima a inda aka shuka shi  ba tare da an girbe shi ba, don gudun ka da ya yi tauri. Haka nan, ana  girbe shi ne bayan jijiyarsa ta kai girman kimanin mita 1.8 ko kuma fiye da haka.

Ribar Nawa Manomi Yake Samu?

Bisa binceken da aka yi a kwanakin baya na tsadar farashin noman Karas, an kiyasta cewa kowace kadada daya; ta kai kimanin dala 10,600.

Nawa Ake Kashewa Wajen Noman Karas A Kadada Daya?

Kudaden da ake kashewa ciki har da na hayar gona a kowace Kadada daya, sun kai kimanin dala 4,200 zuwa dala 5,000, inda kuma sarrafa shi a kadada daya ya doshi daga dala 1,500 zuwa dala 2,000


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Noman Gwanda Da Kasuwancinta A Saukake

Next Post

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

Gwamnati Ta Bankado Sunaye 15 Da Ake Zargi Da Hannu A Tallafa Wa Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.